Jama’a barkanmu da juma’a, barkanmu da sake kasancewa tare da wannan shafi na GORON JUMA’A. Shafin dake bawa kowa damar mika sakon gaishe-gaishensa zuwa ga ‘yan’uwa da abokan arziki, na kusa da na nesa, har ma da wadanda aka dade ba a hadu ba.
Kamar kowane mako yau ma shafin na tafe da wasu sakonnin gaishe-gaishen da kuka aiko mana kamar haka;
Sako daga Mu’azzam Salis, Jihar Gombe:
Sakon gaisuwata zuwa ga Amina ‘yar fara, da Hafsat Alkali, da G.boy dan Mama, da Zuhra fashion. Ina gaishe da mahaifiyata da mahaifina, ina yi musu fatan alkhairi.
Sako daga Aliyu Yusif, Tsamiya Babba, Jihar Kano:
Da fari ina gaishe da me gabatar da wannan shafi, sannan ina gaishe da abokina Bashir Ahmad, da daya abokin nawa Kamal Muhammad, da Al’amin Baba. Da fatan za su yi juma’a lafiya.
Sako daga Zainab Zeey Iliyas, Jihar Kaduna:
Ina gaishe da Rabi’at, ina gaishe da Nafisa, da kuma Aisha, da Fatima da Maryam, da Khadija, da Habiba, da duk sauran kawayena, ina yi musu barka da juma’a, da fatan za a yi sallar juma’a lafiya.
Sako daga Nabila Yahaya, Jihar Kano:
Sakona zuwa ga kannena Ummi Yahaya, Na’ima Yahaya, Suwaiba Yahaya, Umar Yahaya, da kuma yayyena kamar su; Anti Hauwa, Anti Hafsa, Yaya Aminu, da kuma Iyayenmu bakidaya ina gaishe su da kawayena na makarantar Islamaiyya da kuma boko.














Discussion about this post