ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar Ya Koma APC

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Atiku

Abubakar Atiku Abubakar, ɗan tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki, inda ya bayyana aniyarsa ta yin aiki domin sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2027.

Ɗan Atikun, Wanda aka fi sani da “Abba”, an tarɓe shi a ranar Alhamis a Majalisar Tarayya da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, tare da manyan shugabannin APC daga shiyyar Arewa maso Gabas.

  • Atiku Ya Fara Neman Mulki Tun Ina NYSC – Datti Baba-Ahmed
  • Barau Ya Gargaɗi Gwamna Abba Kan Siyasantar Da Batun Tsaro A Kano

Da yake sanar da sauya sheƙarsa, Abba ya ce ya yi murabus daga jam’iyyar PDP, ya kuma yanke shawarar shiga APC bisa abin da ya kira kyakkyawan jagoranci da tsare-tsaren gwamnatin Shugaba Tinubu. Ya ce zai yi aiki tare da Sanata Barau domin tabbatar da wa’adin mulki na biyu ga Tinubu a 2027, tare da umartar dukkan mambobin ƙungiyarsa su shiga APC su goyi bayan Ajandar “Renewed Hope”.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bayyana cewa ƙungiyarsa ta siyasa da ya kafa a 2022, wato Haske Atiku Organisation, za ta sauya suna nan take zuwa Haske Bola Tinubu Organisation, alamar cikakken daidaituwar manufofin APC gabanin zaɓen 2027. Shugaban APC na ƙasa mai kula da Arewa maso Gabas, Comrade Mustapha Salihu, ya bayyana wannan sauyin sheƙa a matsayin alama mai nuni da  tabbatar ƙasa kyawawan manufofin APC.

A nasa jawabin, Sanata Barau Jibrin ya taya Abba murna bisa matakin da ya kira jarumta da hikima, yana mai cewa ya yanke wannan shawara ne bisa aƙida da imani da manufofin Shugaba Tinubu. Ya ƙara da cewa Abba, wanda ya kasance yana bibiyar siyasar Nijeriya daga Amurka, ya dawo ne domin ba da gudummawa wajen gina makomar ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

A ƙarshe, wakilan ƙungiyarsa daga Kano sun tabbatar da cewa za su ƙara zage damtse wajen tallata APC da tabbatar da nasararta a zaɓen 2027.

Atiku
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na Cgtn: Duniya Na Maraba Da Shawarar Sin a Bangaren Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

Binciken Jin Ra'ayin Jama'a Na Cgtn: Duniya Na Maraba Da Shawarar Sin a Bangaren Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.