Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya buƙaci masu kamfanin Simintin Ashaka da su gyara hanyoyin da manyan motocin da ke kai da dawo da siminti da sauran kayayyaki suka lalata.
Gwamnan ya yi wannan kiran ne ranar Litinin lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin kamfanin HBM Nigeria Plc, ƙarƙashin jagorancin Babban Daraktan Kamfanin, Lolu Alade-Akinyemi, a gidan gwamnati da ke Gombe.
Yahaya ya ce duk da cewa kamfanin na da haƙƙin faɗaɗa kasuwancinsa da samun riba, ya kamata ya kula da jin daɗin al’ummomin da ke kusa da kamfanin da kuma muhalli.
Ya ce wasu hanyoyin da gwamnatin jihar ta gina sun lalace sakamakon yawan amfani da manyan motocin kamfanin.
Gwamnan ya kuma ce shirin ƙara yawan samar da siminti na Ashaka zuwa tan miliyan biyu a shekara zai samar da ƙarin ayyukan yi tare da bunƙasa tattalin arziƙin Gombe.
Alade-Akinyemi ya ce HBM Nigeria na nan daram kan ƙudurinsa na taimaka wa Gombe, musamman wajen samar da ayyukan yi, bunƙasa al’umma da kuma samar da ayyukan jin daɗin jama’a.














