Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da aiwatar da sabon tsarin albashi ga dukkanin ma’aikata masu koyarwa da waɗanda ba sa koyarwa a jami’o’in jihar guda biyu; wato Aliko Dangote University of Science and Technology da ke garin Wudil, da kuma Northwest University da ke birnin Kano, a ranar Litinin, 10 ga watan Agusta, 2026.
Wannan muhimmiyar sanarwa ta fito ne ta bakin Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, inda ya bayyana cewa an yi amfani da sabon tsarin ƙarin albashin ne daidai da wanda Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar a jami’o’inta da ke faɗin Nijeriya domin inganta jin daɗin ma’aikata.
Kamar yadda cikakken bayanin ya tabbatar, Gwamna Yusuf ya ɗauki wannan mataki ne biyo bayan karɓar rahoton wani kwamiti na musamman da Majalisar Zartarwa ta Jihar Kano ta kafa, domin yin nazari a kan buƙatar jami’o’in guda biyu na daidaita tsarinsu da sabon ƙarin albashin ƙasa.
A ƙarƙashin wannan tsari da aka amince da shi, za a fara lissafin sabon albashin ne tun daga watan Janairun 2026, yayin da za a fara raba kuɗaɗen a hukumance ga ma’aikatan a watan Satumbar 2026. Tsarin zai lashe jimillar naira miliyan 391.8 a kowane wata, wanda ya kama kusan naira biliyan 4.7 a duk shekara ga jami’o’in biyu.
Bugu da ƙari, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudurinsa na tabbatar da kyakkyawan yanayin aiki ga ma’aikata, inda ya kuma bayar da amincewa wajen kafa kwamitocin ziyara (Visitation Panels) a makarantun biyu da sauran manyan makarantun jihar Kano, domin ƙarfafa bin ƙa’ida, da kyakkyawan shugabanci da kiyaye asusun makarantun.














