Bincike na al’umma da ci gaban birane ya nuna yadda birnin Kano da ke Arewa maso Yammacin Nijeriya ya samu fitowa a matsayin birni na 9 a jerin birane mafi yawan jama’a a duk faɗin duniya, sakamakon ƙaruwar al’umma da karɓuwar kasuwanci tsawon shekaru.
Rahoton da Jaridar Daily Trust ta rawaito ya nuna cewa, cibiyar nazarin al’umma ta duniya ta gudanar da bincike inda aka gano cewa saurin haɓakar tattalin arziƙi, da kasuwanci, da hada-hadar kayayyaki a kasuwanni irin su Kurmi da Kantin Kwari sun zama tamkar fitilar da ke jan hankalin mutane daga sauran jihohi da ƙasashe makwabtaka zuwa birnin.
Hukumar kula da al’umma da walwala ta bayyana cewa tsarin zamantakewa, da wadatar abinci daga karkara, da kuma yadda birnin yake a matsayin cibiyar ilimi da addini a yankin yammacin Afirka, duk sun taimaka wajen haɓaka yawan mazauna birnin gaba ɗaya.
Masana harkokin ci gaban birane sun jaddada cewa wannan ƙaruwa ta haifar da buƙatar haɓaka ayyukan shimfiɗa tsarin tafiyar da ababen hawa, da kyautata harkokin lafiya, da kuma faɗaɗa tsarin gidaje domin magance matsalolin da ke tattare da karɓar ɗimbin jama’a.














