Sojojin Nijeriya sun gano tare da rusa wasu masana’antun ƙera makamai guda biyu ba bisa ƙa’ida ba a Vom da ke ƙaramar hukumar Jos ta Kudu a Jihar Filato, inda suka kama mutane biyar tare da ƙwato makamai da kayan aikin ƙere-ƙere masu yawa.
An gudanar da sumamen ne ranar Alhamis ta hannun dakarun Rundunar Gaggawa ƙarƙashin Operation Enduring Peace, a wani ɓangare na ƙoƙarin daƙile yaɗuwar haramtattun makamai a yankin.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar haɗin gwuiwa, Kyaftin Chinonso Polycarp Oteh, ya fitar ranar Juma’a, ya ce an kai sumamen ne bayan tattara bayanan sirri da kuma sa ido na musamman da aka gudanar cikin sirri.
Sanarwar ta ce an kama waɗanda ake zargin ne yayin da suke ƙera makamai, inda aka ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda tara da aka kera a gida, da bindiga ƙirar pistol guda ɗaya, mujallun AK-47 guda huɗu marasa harsashi, da wasu sassan bindigogi da dama tare da harsasai da kayan aikin walda da huda ƙarafa.
Rundunar ta bayyana cewa ana ci gaba da bincike kan waɗanda aka kama tare da gudanar da ƙarin sumame domin ƙwace sauran makamai da ake zargin suna hannun masu laifi, yayin da ta buƙaci al’umma da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai kan duk wani kai kawo da ba a gamsu da shi ba.
















Discussion about this post