ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta Sayar Wa Da Manoma Takin Zamani Kan Farashi Mai Rahusa

by Abubakar Abba
2 months ago
Taki

Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da cewa, a kakar noman bana ta 2026, za ta sayar wa da manoman jihar takin zamani a kan farashin naira 25,000 duk buhu guda.

Sayen takin dai a jihar, ya kasance wani babban kalubale da manoman jihar suke fuskanta, inda kuma a gefe daya, jihar ke ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro.

A kakar daminar 2026, manoman sun sayi takin a kan duk buhu daya naira 45,000, saboda samun inganta lamarin tsaro a jihar, wanda hakan ya sa manoman jihar suka yi noma mai yawa.

ADVERTISEMENT

Usman Abdul, wani manomi a Karamar Hukumar Kankia a jihar, ya danganta matakin da gwamnatin jihar ta dauka, na sayar wa da manoman jihar buhun takin zamani kan farashin naira 25,000, a matsayin samar da masu sauki ga sana’ar tasu.

Sai dai, ya nuna damuwarsa, a kan sake dawowar ayyukan ‘yan bidiga a wasu sassan jihar, wanda ya ce; hakan zai iya dawo da hannun agogo baya.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Kwamishinan ma’aiktar aikin noma na jihar, Aliyu Lawal Shargalle, ya bayyana cewa; majalisar zartwarwa ta jihar ce ta amince da sayo tan 20,000 na takin zamanin, wanda ya kai daidai da buhu 400,000.

Ya ce, takin ya hada da samfurin NPK 20:10:10, NPK 15:15:15, da urea, domin yin noman na 2026, inda ya kara da cewa; gwamnatin za ta sayar da takin ga manoman a kan farashi mai sauki.

“Gwamnatin ta samar da wannan daukin ne, domin tabbatar da ganin an samar da ingantaccen takin, kuma a kan lokaci tare da sayar musu da shi kan farashi mai sauki,” in ji kwamishinan.

Ya kara da cewa, hakan zai kuma sanya a kara samar da wadataccen abinci a jihar tare da kuma ci gaba da kokarin gwamnatin na kara inganta rayuwar manoman jihar.

Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen jihar, wato AFAN, Alhaji Ya’u Umar Gwajo-gwajo, ya bayyana cewa; kungiyar tare da hadaka da gwamnatin jihar, ta samar da tsarin da za a yi amfani da shi wajen rabar da takin, musamman domin tabbatar da an yi gaskiya da kuma bin ka’idar da ta dace.

 A cewarsa, za a rabar takin a mazabun da ke jihar, domin tabbatar da cewa; takin ya kai ga ainahin manoma na gaskiya.

Kazalika, Gwajo-gwajo ya sanar da cewa; kungiyar na ci gaba da nuna damuwarta, kan ci gaba da afkuwar hare-haren ‘yan bindiga a jihar.

Koda-yake, ya kara da cewa; gwamnatin jihar ta bai wa manoma tabbacin cewa; za ta yi dukkan mai yiwuwa, domin kara bunkasa fannin tsaron jihar, musamman domin manoman su samu damar komawa su ci gaba da noma a gonakinsu.

Ya sanar da cewa, gwamnatin jihar ta kuma sayo ingantaccen Irin noma da za ta raba wa manoman jihar.

Ya ce, hakan na daya daga cikin kokarin da gwamnatin ke ci gaba da yi, na kara habaka fannin aikin noma na jihar da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar.

Ya kara da cewa, gwamnatin jihar, ta dauki matakan da suka kamata, domin ganin cewa; manoman sun yi amfani da daukin na takin yadda ya dace da manoman jihar, sun gamsu da matakan da gwamnatin jihar ke ci gaba da dauka.

Taki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
An Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Wutar Lantarki Zuwa 400MW Da Gwamnatin Legas

An Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Wutar Lantarki Zuwa 400MW Da Gwamnatin Legas

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.