Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da cewa, a kakar noman bana ta 2026, za ta sayar wa da manoman jihar takin zamani a kan farashin naira 25,000 duk buhu guda.
Sayen takin dai a jihar, ya kasance wani babban kalubale da manoman jihar suke fuskanta, inda kuma a gefe daya, jihar ke ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro.
A kakar daminar 2026, manoman sun sayi takin a kan duk buhu daya naira 45,000, saboda samun inganta lamarin tsaro a jihar, wanda hakan ya sa manoman jihar suka yi noma mai yawa.
Usman Abdul, wani manomi a Karamar Hukumar Kankia a jihar, ya danganta matakin da gwamnatin jihar ta dauka, na sayar wa da manoman jihar buhun takin zamani kan farashin naira 25,000, a matsayin samar da masu sauki ga sana’ar tasu.
Sai dai, ya nuna damuwarsa, a kan sake dawowar ayyukan ‘yan bidiga a wasu sassan jihar, wanda ya ce; hakan zai iya dawo da hannun agogo baya.
Kwamishinan ma’aiktar aikin noma na jihar, Aliyu Lawal Shargalle, ya bayyana cewa; majalisar zartwarwa ta jihar ce ta amince da sayo tan 20,000 na takin zamanin, wanda ya kai daidai da buhu 400,000.
Ya ce, takin ya hada da samfurin NPK 20:10:10, NPK 15:15:15, da urea, domin yin noman na 2026, inda ya kara da cewa; gwamnatin za ta sayar da takin ga manoman a kan farashi mai sauki.
“Gwamnatin ta samar da wannan daukin ne, domin tabbatar da ganin an samar da ingantaccen takin, kuma a kan lokaci tare da sayar musu da shi kan farashi mai sauki,” in ji kwamishinan.
Ya kara da cewa, hakan zai kuma sanya a kara samar da wadataccen abinci a jihar tare da kuma ci gaba da kokarin gwamnatin na kara inganta rayuwar manoman jihar.
Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen jihar, wato AFAN, Alhaji Ya’u Umar Gwajo-gwajo, ya bayyana cewa; kungiyar tare da hadaka da gwamnatin jihar, ta samar da tsarin da za a yi amfani da shi wajen rabar da takin, musamman domin tabbatar da an yi gaskiya da kuma bin ka’idar da ta dace.
A cewarsa, za a rabar takin a mazabun da ke jihar, domin tabbatar da cewa; takin ya kai ga ainahin manoma na gaskiya.
Kazalika, Gwajo-gwajo ya sanar da cewa; kungiyar na ci gaba da nuna damuwarta, kan ci gaba da afkuwar hare-haren ‘yan bindiga a jihar.
Koda-yake, ya kara da cewa; gwamnatin jihar ta bai wa manoma tabbacin cewa; za ta yi dukkan mai yiwuwa, domin kara bunkasa fannin tsaron jihar, musamman domin manoman su samu damar komawa su ci gaba da noma a gonakinsu.
Ya sanar da cewa, gwamnatin jihar ta kuma sayo ingantaccen Irin noma da za ta raba wa manoman jihar.
Ya ce, hakan na daya daga cikin kokarin da gwamnatin ke ci gaba da yi, na kara habaka fannin aikin noma na jihar da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar.
Ya kara da cewa, gwamnatin jihar, ta dauki matakan da suka kamata, domin ganin cewa; manoman sun yi amfani da daukin na takin yadda ya dace da manoman jihar, sun gamsu da matakan da gwamnatin jihar ke ci gaba da dauka.















Discussion about this post