ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta Sayar Wa Da Manoma Takin Zamani Kan Farashi Mai Rahusa

by Abubakar Abba
2 months ago
Taki

Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da cewa, a kakar noman bana ta 2026, za ta sayar wa da manoman jihar takin zamani a kan farashin naira 25,000 duk buhu guda.

Sayen takin dai a jihar, ya kasance wani babban kalubale da manoman jihar suke fuskanta, inda kuma a gefe daya, jihar ke ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro.

A kakar daminar 2026, manoman sun sayi takin a kan duk buhu daya naira 45,000, saboda samun inganta lamarin tsaro a jihar, wanda hakan ya sa manoman jihar suka yi noma mai yawa.

ADVERTISEMENT

Usman Abdul, wani manomi a Karamar Hukumar Kankia a jihar, ya danganta matakin da gwamnatin jihar ta dauka, na sayar wa da manoman jihar buhun takin zamani kan farashin naira 25,000, a matsayin samar da masu sauki ga sana’ar tasu.

Sai dai, ya nuna damuwarsa, a kan sake dawowar ayyukan ‘yan bidiga a wasu sassan jihar, wanda ya ce; hakan zai iya dawo da hannun agogo baya.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Kwamishinan ma’aiktar aikin noma na jihar, Aliyu Lawal Shargalle, ya bayyana cewa; majalisar zartwarwa ta jihar ce ta amince da sayo tan 20,000 na takin zamanin, wanda ya kai daidai da buhu 400,000.

Ya ce, takin ya hada da samfurin NPK 20:10:10, NPK 15:15:15, da urea, domin yin noman na 2026, inda ya kara da cewa; gwamnatin za ta sayar da takin ga manoman a kan farashi mai sauki.

“Gwamnatin ta samar da wannan daukin ne, domin tabbatar da ganin an samar da ingantaccen takin, kuma a kan lokaci tare da sayar musu da shi kan farashi mai sauki,” in ji kwamishinan.

Ya kara da cewa, hakan zai kuma sanya a kara samar da wadataccen abinci a jihar tare da kuma ci gaba da kokarin gwamnatin na kara inganta rayuwar manoman jihar.

Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen jihar, wato AFAN, Alhaji Ya’u Umar Gwajo-gwajo, ya bayyana cewa; kungiyar tare da hadaka da gwamnatin jihar, ta samar da tsarin da za a yi amfani da shi wajen rabar da takin, musamman domin tabbatar da an yi gaskiya da kuma bin ka’idar da ta dace.

 A cewarsa, za a rabar takin a mazabun da ke jihar, domin tabbatar da cewa; takin ya kai ga ainahin manoma na gaskiya.

Kazalika, Gwajo-gwajo ya sanar da cewa; kungiyar na ci gaba da nuna damuwarta, kan ci gaba da afkuwar hare-haren ‘yan bindiga a jihar.

Koda-yake, ya kara da cewa; gwamnatin jihar ta bai wa manoma tabbacin cewa; za ta yi dukkan mai yiwuwa, domin kara bunkasa fannin tsaron jihar, musamman domin manoman su samu damar komawa su ci gaba da noma a gonakinsu.

Ya sanar da cewa, gwamnatin jihar ta kuma sayo ingantaccen Irin noma da za ta raba wa manoman jihar.

Ya ce, hakan na daya daga cikin kokarin da gwamnatin ke ci gaba da yi, na kara habaka fannin aikin noma na jihar da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar.

Ya kara da cewa, gwamnatin jihar, ta dauki matakan da suka kamata, domin ganin cewa; manoman sun yi amfani da daukin na takin yadda ya dace da manoman jihar, sun gamsu da matakan da gwamnatin jihar ke ci gaba da dauka.

Taki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
An Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Wutar Lantarki Zuwa 400MW Da Gwamnatin Legas

An Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Wutar Lantarki Zuwa 400MW Da Gwamnatin Legas

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.