ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Katsina Za Ta Sayar Wa Da Manoma Takin Zamani Kan Farashi Mai Rahusa

by Abubakar Abba
1 month ago
Taki

Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da cewa, a kakar noman bana ta 2026, za ta sayar wa da manoman jihar takin zamani a kan farashin naira 25,000 duk buhu guda.

Sayen takin dai a jihar, ya kasance wani babban kalubale da manoman jihar suke fuskanta, inda kuma a gefe daya, jihar ke ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro.

A kakar daminar 2026, manoman sun sayi takin a kan duk buhu daya naira 45,000, saboda samun inganta lamarin tsaro a jihar, wanda hakan ya sa manoman jihar suka yi noma mai yawa.

ADVERTISEMENT

Usman Abdul, wani manomi a Karamar Hukumar Kankia a jihar, ya danganta matakin da gwamnatin jihar ta dauka, na sayar wa da manoman jihar buhun takin zamani kan farashin naira 25,000, a matsayin samar da masu sauki ga sana’ar tasu.

Sai dai, ya nuna damuwarsa, a kan sake dawowar ayyukan ‘yan bidiga a wasu sassan jihar, wanda ya ce; hakan zai iya dawo da hannun agogo baya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Kwamishinan ma’aiktar aikin noma na jihar, Aliyu Lawal Shargalle, ya bayyana cewa; majalisar zartwarwa ta jihar ce ta amince da sayo tan 20,000 na takin zamanin, wanda ya kai daidai da buhu 400,000.

Ya ce, takin ya hada da samfurin NPK 20:10:10, NPK 15:15:15, da urea, domin yin noman na 2026, inda ya kara da cewa; gwamnatin za ta sayar da takin ga manoman a kan farashi mai sauki.

“Gwamnatin ta samar da wannan daukin ne, domin tabbatar da ganin an samar da ingantaccen takin, kuma a kan lokaci tare da sayar musu da shi kan farashi mai sauki,” in ji kwamishinan.

Ya kara da cewa, hakan zai kuma sanya a kara samar da wadataccen abinci a jihar tare da kuma ci gaba da kokarin gwamnatin na kara inganta rayuwar manoman jihar.

Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa reshen jihar, wato AFAN, Alhaji Ya’u Umar Gwajo-gwajo, ya bayyana cewa; kungiyar tare da hadaka da gwamnatin jihar, ta samar da tsarin da za a yi amfani da shi wajen rabar da takin, musamman domin tabbatar da an yi gaskiya da kuma bin ka’idar da ta dace.

 A cewarsa, za a rabar takin a mazabun da ke jihar, domin tabbatar da cewa; takin ya kai ga ainahin manoma na gaskiya.

Kazalika, Gwajo-gwajo ya sanar da cewa; kungiyar na ci gaba da nuna damuwarta, kan ci gaba da afkuwar hare-haren ‘yan bindiga a jihar.

Koda-yake, ya kara da cewa; gwamnatin jihar ta bai wa manoma tabbacin cewa; za ta yi dukkan mai yiwuwa, domin kara bunkasa fannin tsaron jihar, musamman domin manoman su samu damar komawa su ci gaba da noma a gonakinsu.

Ya sanar da cewa, gwamnatin jihar ta kuma sayo ingantaccen Irin noma da za ta raba wa manoman jihar.

Ya ce, hakan na daya daga cikin kokarin da gwamnatin ke ci gaba da yi, na kara habaka fannin aikin noma na jihar da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar.

Ya kara da cewa, gwamnatin jihar, ta dauki matakan da suka kamata, domin ganin cewa; manoman sun yi amfani da daukin na takin yadda ya dace da manoman jihar, sun gamsu da matakan da gwamnatin jihar ke ci gaba da dauka.

Taki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
An Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Wutar Lantarki Zuwa 400MW Da Gwamnatin Legas

An Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Wutar Lantarki Zuwa 400MW Da Gwamnatin Legas

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.