Wasu ƴan bindiga sun kashe Hakimin Gundumar Gwande da ke ƙaramar hukumar Bokkos a Jihar Filato, Saf Samuel Alaket, bayan sun yi masa kwanton ɓauna a yammacin ranar Talata.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:30 na dare a kusa da iyakar Sha da Daffo a ƙaramar hukumar Bokkos. Rahotanni daga yankin sun ce marigayin na kan hanyarsa ta komawa gida daga kasuwar Daffo ta ranar Talata lokacin da maharan suka tare motarsa tare da buɗe mata wuta.
An ruwaito cewa tun da farko Alaket ya halarci taron majalisar sarakunan gargajiya a Bokkos kafin ya kama hanyar komawa gida. Shaidu sun ce ya samu munanan raunukan harbin bindiga a yayin harin.
An garzaya da shi zuwa wani asibiti da ke kusa domin ceto rayuwarsa, amma daga bisani ya rasu sakamakon raunukan da ya samu.
Wani mazaunin yankin, Aten Pukat, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana marigayin a matsayin shugaba mai kishin zaman lafiya da ci gaban al’ummarsa.
Ya ce mutuwarsa babban rashi ne ga al’ummar Gwande da ɗaukacin yankin Bokkos, yayin da lamarin ya jefa majalisar sarakunan gargajiya da mazauna yankin cikin alhini.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, rundunar ƴansandan Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan lamarin, domin ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar, Alfred Alabo ba.















Discussion about this post