ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wuta Ta Ƙone Miji, Mata Da Ƴaƴansu Ƙurmus A Katsina

by Sani Anwar
7 months ago
wuta

Wata gobara da ta tashi da sanyin safiyar ranar Litinin, ta yi sanadiyar mutuwar mutum biyar tare da lalata dukiyoyi na miliyoyin nairori a Ƙauyen Kofar Sauri da ke cikin birnin Katsina.

Muhammad Habibu mai shekara 35 da matarsa Fatima Muhammad da ‘ya’yansu uku, Khadija, Abubakar da Aliyu, dukkanninsu sun ƙone ƙurmus.

  • Gobara Ta Yi Ajalin Mutum 5 ‘Yan Gida Ɗaya A Jihar Katsina
  • Hukuma Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Wuta A Lokacin Hunturu A Kano

Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Muhammad Habibu, ma’aikaci ne a hukumar ruwa ta Jihar Katsina, har zuwa rasuwarsa.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa, har yanzu ba a tantance ainihin musabbabin tashin gobarar ba, mazauna yankin na zargin tashin wutar a lokacin da aka dawo da wutar lantarki a yankin.

Har ila yau, gobarar ta tashi ne daga falo tare da bazuwa cikin sauri zuwa sauran ɗakuna yayin da suke tsaka da yin barci.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Wani ɗan’uwan waɗanda abin ya shafa mai suna Kasim Aliyu ya ce, da misalin ƙarfe 3:00 na dare ya ji muryar wata mata daga nesa tana faɗin; “Innalillahi wa inna ilaihir raji’un”, (Haƙiƙa ga Allah muke, kuma gare shi za mu koma).

Da farko, ya yi tunanin al’ada ce wadda aka saba yi, har sai zuwa ƙarfe 3:30 na dare, lokacin da ya hango wani abu mai kama da wuta na tashi.

Kasim ya ƙara da cewa, “Mai gidan, yayana ne; ubanmu ɗaya da shi, gobarar ta ƙone gidan da ne misalin ƙarfe 3:00 na dare, sai na hango wani abu a lokacin, amma ban san ko mene ne ba, har sai da aka kira ni da misalin ƙarfe 4:00 na dare, inda aka sanar da ni cewa; yayana da iyalansa baki-ɗaya sun mutu sanadiyyar gobara, Allah ya gafarta musu, ya ba su Aljannar Firdausi.

Shedun gani da ido sun bayyana cewa, duk da ƙoƙarin da maƙwabta da sauran waɗanda suka kai ɗauki suka yi, amma abin ya ci tura. Duk da dai, sun koka da yadda jami’an hukumar kashe gobara ta Jihar Katsina suka zo a makare, ba tare da kuma yin wani abin a zo a gani ba.

Wani daga cikin maƙwabtan mamacin mai suna Musa Hamza ya ce, “Ina da yaƙinin cewa, lokacin da hukumar kashe gobara ta zo, tuni mutanen gidan sun riga sun mutu, duk da cewa; sun yi iya ƙoƙarinsu wajen ganin sun kashe wutar, amma ba su iya yin nasarar ceto mamatan ba.

Shi ma, guda daga cikin maƙwabtan, Magaji Bala, ya koka kan yadda mazauna garin sukan kwana ba tare da wutar lantarki ba, sai dai yanayin yadda ake kawo wutar lantarkin, yakan haifar da ɓarna a duk lokacin da wutar ta dawo.

“Wannan lamari yana faruwa a wasu sassa na cikin birnin Katsina, a kwanakin baya ma; makamancin hakan ya kusan faruwa, don haka; akwai buƙatar yin taka-tsan-tsan a tsakanin mazauna wannan gari,” inji shi.

Da aka tuntubi babban jami’in kashe gobara na hukumar kashe gobara ta Jihar Katsina, Rabe Audi Kurmuyal, ya tabbatar da cewa; mutanensa ne suka kashe gobarar, saɓanin iƙirarin da ake yin a cewa; ƴan kwana-kwanan sun isa wajen a makare.

Haka zalika, wasu mazauna yankin sun yi zargin cewa; kamfanin rarraba wutar lantarki na (KEDCO), na ci gaba da samun taɓarɓarewa wajen samar da wutar lantarki, inda suka ce; yawan katsewar wutar lantarkin akai-akai da kuma dawo da ita ne musabbabin lalata na’urorin lantarkin.

Da take jajanta wa iyalai da abokan arziƙi da maƙwaftan waɗanda abin ya shafa, Sakatariyar Zartarwa ta Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Katsina (SEMA), Binta Hussaini Dangani, ta bayyana faruwar lamarin a matsayin wani iftila’i daga Allah SWT, sannan ta yi addu’ar Allah ya gafarta wa waɗanda suka rasu ya kuma sanya su cikin Aljanna Firdausi.

Dangani, wadda ta isa wurin mintuna kaɗan bayan faruwar lamarin, ta yi addu’ar Allah ya kawo mana ƙarshen wannan bala’i tare da bayar da tabbacin cewa, gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa iyalan waɗanda abin ya shafa. Sannan, ta shawarci mazauna garin, da su riƙa tabbatar da kashe kayan wutan lantarki a koda-yaushe kafin su kwanta barci tare da kula da harkokin da suka shafi wuta.

Ta ƙara da cewa, tuni ma’aikatan SEMA sun gudanar da tantance irin ɓarnar da wutar ta yi tare da fara shirye-shiryen samar da kayan agaji.

Manajan KEDCO na yankin Katsina, Aminu Bukari, ya ce; da wuya a samu ƙaruwar wutar lantarki wadda za ta shafi gida ɗaya tak a tsakanin gidaje aƙalla sama da 5,000.

wuta
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Game Da Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Tabbatar Da Tsaro A Kasar Habasha

An Yi Taron Kara Wa Juna Sani Game Da Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Tabbatar Da Tsaro A Kasar Habasha

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.