ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Muhimmancin Kimiyya Da Fasaha Ga Ci Gaban Al’ummar Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
Kimiyya

Gwamnatin Tarayya ta yaba wa Al’ummar Duniya kan Fasahar Ilimi (ICEDT) saboda ba da gudunmawarsu wajen ci gaban tsarin ilimi a Nijeriya.

 

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, wanda ya jaddada muhimmancin fasaha wajen tsara makomar kasa a fannin ilimi, ya bayyana haka ne yayin da ma’aikatar ta kaddamar da matakin gwaji na shirin horar da ‘Malaman kan Fasahar Wucin Gadi (AI)’.

ADVERTISEMENT
  • Ƙungiyar IPOB Ta Yi Watsi Da Hukuncin Ɗaurin Rai-Da-Rai Ga Nnamdi Kanu
  • Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba

A jawabin da ya yi ranar Talata a Abuja a wajen bikin kaddamar da shirin gwamnati da kuma babban mataki a kokarin da ake yi na daidaita koyarwa da koyo da bukatun tattalin arzikin dijital na karni na 21, Alausa ya ce gudunmawar da ake bayarwa, wacce take nufin horar da malamai da basira da kwarewa wajen hada mafita ta AI cikin tsarin ilimi na Nijeriya, duk yabon da za a yi musu ba zai wadatar ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

An wakilce shi ta Sakatare, Mista Abel Enitan, Alausa ya bayyana cewa malaman Kwalejojin Tarayya na Hadin Kai, wadanda su ne farko da za su amfana, suna da matsayi na musamman da na dabaru a fannin ilimi na kasa, saboda haka suna wakiltar ka’idojin inganci, daidaito da kirkire-kirkire.

 

Ya ce: “Ina karfafar duk mahalarta da su shiga cikin horon cikin himma saboda ana sa ran matakin gwaji zai samar da rahotanni da za su jagoranci fadada shirin zuwa dukkan yankunan siyasa guda shida.

 

“Wannan shiri wata kofa ce ta ci gaban fasaha a fannin ilimi a duk fadin kasa, kuma ina kira ga malamai su yi amfani da wannan dama sosai domin su zama zakakuran da za su yada ilimin AI a fannin ilimi ga sauran abokan aikinsu.”

 

A jawabinta, Daraktar Sashen Tallafin Ilimi, Mrs. Larai Nana Ahmed, wacce Mataimakiyar Darakta na Sashen Tallafin Makarantu, Mrs. Ogbuke Njideka Dorothy ta wakilta, ta maimaita jajircewar ma’aikatar wajen hade fasahar dijital cikin bangaren ilimi.

 

Ta bayyana cewa shirin ya dace da Dabarun Fasahar Ilimi na Kasa (National EdTech Strategy) da kuma hangen nesa na Gwamnatin Tarayya na shiryawa dalibai don fuskantar gaskiyar tattalin arzikin dijital.

 

A cewarta, malamai su ne zuciyar wannan sauyi, shi ya sa aka yanke shawarar fara horon da Kwalejojin Tarayya na Hadin Kai, wadanda ke zama fitilar ilimi na sakandare a Nijeriya.

 

A yayin isar da sakon fatan alheri, Shugaban Huldar Dabaru da Masanin Koyo a ICEDT, Dr. Abdurrahman Orasanye, ya bayyana wannan shiri a matsayin muhimmin mataki a tafiyar hadin gwiwa na sauya ilimi ta hanyar kirkire-kirkire.

 

Ya sake tabbatar da jajircewar ICEDT wajen tallafa wa Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki wajen horar da malamai Nijeriya da kwarewar da ake bukata domin samun nasara a duniya mai amfani da fasahar dijital.

Kimiyya
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Kimiyya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Nijeriya, Ghana Da Cote d’Ivoire Za Su Iya Karɓar Baƙincin Gasar Kofin Duniya – Ministan Wasanni Na Ghana

Nijeriya, Ghana Da Cote d'Ivoire Za Su Iya Karɓar Baƙincin Gasar Kofin Duniya - Ministan Wasanni Na Ghana

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.