ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Muhimmancin Kimiyya Da Fasaha Ga Ci Gaban Al’ummar Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 months ago
Kimiyya

Gwamnatin Tarayya ta yaba wa Al’ummar Duniya kan Fasahar Ilimi (ICEDT) saboda ba da gudunmawarsu wajen ci gaban tsarin ilimi a Nijeriya.

 

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, wanda ya jaddada muhimmancin fasaha wajen tsara makomar kasa a fannin ilimi, ya bayyana haka ne yayin da ma’aikatar ta kaddamar da matakin gwaji na shirin horar da ‘Malaman kan Fasahar Wucin Gadi (AI)’.

ADVERTISEMENT
  • Ƙungiyar IPOB Ta Yi Watsi Da Hukuncin Ɗaurin Rai-Da-Rai Ga Nnamdi Kanu
  • Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba

A jawabin da ya yi ranar Talata a Abuja a wajen bikin kaddamar da shirin gwamnati da kuma babban mataki a kokarin da ake yi na daidaita koyarwa da koyo da bukatun tattalin arzikin dijital na karni na 21, Alausa ya ce gudunmawar da ake bayarwa, wacce take nufin horar da malamai da basira da kwarewa wajen hada mafita ta AI cikin tsarin ilimi na Nijeriya, duk yabon da za a yi musu ba zai wadatar ba.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

An wakilce shi ta Sakatare, Mista Abel Enitan, Alausa ya bayyana cewa malaman Kwalejojin Tarayya na Hadin Kai, wadanda su ne farko da za su amfana, suna da matsayi na musamman da na dabaru a fannin ilimi na kasa, saboda haka suna wakiltar ka’idojin inganci, daidaito da kirkire-kirkire.

 

Ya ce: “Ina karfafar duk mahalarta da su shiga cikin horon cikin himma saboda ana sa ran matakin gwaji zai samar da rahotanni da za su jagoranci fadada shirin zuwa dukkan yankunan siyasa guda shida.

 

“Wannan shiri wata kofa ce ta ci gaban fasaha a fannin ilimi a duk fadin kasa, kuma ina kira ga malamai su yi amfani da wannan dama sosai domin su zama zakakuran da za su yada ilimin AI a fannin ilimi ga sauran abokan aikinsu.”

 

A jawabinta, Daraktar Sashen Tallafin Ilimi, Mrs. Larai Nana Ahmed, wacce Mataimakiyar Darakta na Sashen Tallafin Makarantu, Mrs. Ogbuke Njideka Dorothy ta wakilta, ta maimaita jajircewar ma’aikatar wajen hade fasahar dijital cikin bangaren ilimi.

 

Ta bayyana cewa shirin ya dace da Dabarun Fasahar Ilimi na Kasa (National EdTech Strategy) da kuma hangen nesa na Gwamnatin Tarayya na shiryawa dalibai don fuskantar gaskiyar tattalin arzikin dijital.

 

A cewarta, malamai su ne zuciyar wannan sauyi, shi ya sa aka yanke shawarar fara horon da Kwalejojin Tarayya na Hadin Kai, wadanda ke zama fitilar ilimi na sakandare a Nijeriya.

 

A yayin isar da sakon fatan alheri, Shugaban Huldar Dabaru da Masanin Koyo a ICEDT, Dr. Abdurrahman Orasanye, ya bayyana wannan shiri a matsayin muhimmin mataki a tafiyar hadin gwiwa na sauya ilimi ta hanyar kirkire-kirkire.

 

Ya sake tabbatar da jajircewar ICEDT wajen tallafa wa Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki wajen horar da malamai Nijeriya da kwarewar da ake bukata domin samun nasara a duniya mai amfani da fasahar dijital.

Kimiyya
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Kimiyya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Nijeriya, Ghana Da Cote d’Ivoire Za Su Iya Karɓar Baƙincin Gasar Kofin Duniya – Ministan Wasanni Na Ghana

Nijeriya, Ghana Da Cote d'Ivoire Za Su Iya Karɓar Baƙincin Gasar Kofin Duniya - Ministan Wasanni Na Ghana

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.