ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Muhimmancin Kimiyya Da Fasaha Ga Ci Gaban Al’ummar Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
Kimiyya

Gwamnatin Tarayya ta yaba wa Al’ummar Duniya kan Fasahar Ilimi (ICEDT) saboda ba da gudunmawarsu wajen ci gaban tsarin ilimi a Nijeriya.

 

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, wanda ya jaddada muhimmancin fasaha wajen tsara makomar kasa a fannin ilimi, ya bayyana haka ne yayin da ma’aikatar ta kaddamar da matakin gwaji na shirin horar da ‘Malaman kan Fasahar Wucin Gadi (AI)’.

ADVERTISEMENT
  • Ƙungiyar IPOB Ta Yi Watsi Da Hukuncin Ɗaurin Rai-Da-Rai Ga Nnamdi Kanu
  • Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba

A jawabin da ya yi ranar Talata a Abuja a wajen bikin kaddamar da shirin gwamnati da kuma babban mataki a kokarin da ake yi na daidaita koyarwa da koyo da bukatun tattalin arzikin dijital na karni na 21, Alausa ya ce gudunmawar da ake bayarwa, wacce take nufin horar da malamai da basira da kwarewa wajen hada mafita ta AI cikin tsarin ilimi na Nijeriya, duk yabon da za a yi musu ba zai wadatar ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

An wakilce shi ta Sakatare, Mista Abel Enitan, Alausa ya bayyana cewa malaman Kwalejojin Tarayya na Hadin Kai, wadanda su ne farko da za su amfana, suna da matsayi na musamman da na dabaru a fannin ilimi na kasa, saboda haka suna wakiltar ka’idojin inganci, daidaito da kirkire-kirkire.

 

Ya ce: “Ina karfafar duk mahalarta da su shiga cikin horon cikin himma saboda ana sa ran matakin gwaji zai samar da rahotanni da za su jagoranci fadada shirin zuwa dukkan yankunan siyasa guda shida.

 

“Wannan shiri wata kofa ce ta ci gaban fasaha a fannin ilimi a duk fadin kasa, kuma ina kira ga malamai su yi amfani da wannan dama sosai domin su zama zakakuran da za su yada ilimin AI a fannin ilimi ga sauran abokan aikinsu.”

 

A jawabinta, Daraktar Sashen Tallafin Ilimi, Mrs. Larai Nana Ahmed, wacce Mataimakiyar Darakta na Sashen Tallafin Makarantu, Mrs. Ogbuke Njideka Dorothy ta wakilta, ta maimaita jajircewar ma’aikatar wajen hade fasahar dijital cikin bangaren ilimi.

 

Ta bayyana cewa shirin ya dace da Dabarun Fasahar Ilimi na Kasa (National EdTech Strategy) da kuma hangen nesa na Gwamnatin Tarayya na shiryawa dalibai don fuskantar gaskiyar tattalin arzikin dijital.

 

A cewarta, malamai su ne zuciyar wannan sauyi, shi ya sa aka yanke shawarar fara horon da Kwalejojin Tarayya na Hadin Kai, wadanda ke zama fitilar ilimi na sakandare a Nijeriya.

 

A yayin isar da sakon fatan alheri, Shugaban Huldar Dabaru da Masanin Koyo a ICEDT, Dr. Abdurrahman Orasanye, ya bayyana wannan shiri a matsayin muhimmin mataki a tafiyar hadin gwiwa na sauya ilimi ta hanyar kirkire-kirkire.

 

Ya sake tabbatar da jajircewar ICEDT wajen tallafa wa Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da sauran masu ruwa da tsaki wajen horar da malamai Nijeriya da kwarewar da ake bukata domin samun nasara a duniya mai amfani da fasahar dijital.

Kimiyya
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kimiyya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Nijeriya, Ghana Da Cote d’Ivoire Za Su Iya Karɓar Baƙincin Gasar Kofin Duniya – Ministan Wasanni Na Ghana

Nijeriya, Ghana Da Cote d'Ivoire Za Su Iya Karɓar Baƙincin Gasar Kofin Duniya - Ministan Wasanni Na Ghana

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.