Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa daga yanzu masu neman gurbin karatun NCE da ke da aƙalla credit huɗu ba za su sake rubuta jarabawar share fagen shiga jami’a (UTME) ba.
Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin taron manufofin shiga jami’o’i na shekarar 2026 da JAMB ta shirya a Abuja.
A cewarsa, sabon tsarin na daga cikin gyare-gyaren da gwamnati ke yi domin faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi, musamman a fannin horas da malamai da kuma shirye-shiryen noma da suka shafi aikin gona.
Sai dai ministan ya bayyana cewa duk da cire sharaɗin rubuta UTME, dole ne ɗaliban su yi rajista da JAMB, sannan a tantance takardunsu ta hanyar tsarin rukunin bayanai na CAPS kafin a ba su takardar shiga makaranta.
Alausa ya ƙara da cewa sabon tsarin zai kuma shafi masu neman shiga Diploma ta ƙasa a fannonin aikin gona da kwasa-kwasain da ba na fasaha ba, yana mai cewa matakin zai rage matsin lambar UTME tare da ƙara yawan masu shiga fannin koyarwa da aikin gona waɗanda gwamnati ke ganin suna da muhimmanci ga ci gaban ƙasa.















Discussion about this post