Gwamnonin da aka zaɓa karkashin jam’iyyar APC sun gana da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda suka samu amincewarsa don fara gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyar. Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan kammala taron.
Bago ya ce gwamnonin sun je ne domin gode wa shugaban ƙasa bisa goyon bayan da yake ba su da kuma jam’iyyar APC baki ɗaya. Ya ƙara da cewa Tinubu ya ba su umarni kan yadda za su gudanar da zaɓen fidda gwani bisa dokar zaɓe, ta hanyar sulhu ko kuma zaɓen kai tsaye.
A cewarsa, shugaban ƙasa ya jaddada goyon bayansa ga matakin da gwamnonin suka ɗauka kan tsarin gudanar da zaɓen fidda gwani. “Ya sake tabbatar mana da goyon bayansa, kuma ya ba mu damar ci gaba da aiwatar da tsarin,” in ji Bago.
Ya kuma bayyana cewa tattaunawar ta shafi jadawalin zaɓen fidda gwani da aka riga aka fitar, tare da hanyoyin tabbatar da gaskiya da adalci a tsarin.















Discussion about this post