ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Kafa Asusun Tallafa Wa Tsaro, Kowace Jiha Za Ta Riƙa Bayar Da Biliyan 1 Duk Wata

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
8 months ago
Arewa

A ƙoƙarin ƙungiyar gwamnonin Arewa na yaƙi da matsalolin tsaro da suka addabi yankin, gwamnonin sun amince da samar da Asusun Gidauniyar Tsaro na yanki da suka tsara domin samar da wadataccen kuɗaɗe don ƙarfafa ayyukan tsaro a faɗin yankin Arewa.

 

Sun cimma wannan matsayar ne a yayin zaman haɗin guiwa na musamman tsakanin ƙungiyar gwamnonin jihohin Arewan (NSGF) da Majalisar Sarakunan Arewa wanda ya gudana a Sir Kashim Ibrahim House, Kaduna ranar Litinin.

ADVERTISEMENT
  • Sultan Ya Nemi Gwamnonin Arewa Da Su Riƙa Saurarar Masu Sukarsu
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Sace A Dajin Kogi

Shugaban NSGF kuma Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya shi ne ya jagoranci zaman, wanda aka cimma matsayar cewa kowace jiha daga cikin jihohi 19 da suke faɗin Arewa za su ke bayar da gudunmawar Naira biliyan ɗaya duk wata kuma za a ke cirewa ne kai tsaye bisa tsarin da dukkanin masu ruwa da tsaki suka aminta.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Bayan cire kuɗin kai tsaye zai shiga asusun gidauniyar tsaron da aka samar domin yaƙi da matsalar tsaro ciki har da yaƙi da garkuwa da mutane.

 

Gwamnoni da sarakunan sun nuna cewa wannan matakin ya kamata a ɗauke shi tsawon lokaci domin haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen tunƙarar matsalar tsaro da ya addabi yankin tsawon shekaru.

 

A jawabin bayan taro wanda shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa Muhammadu Inuwa Yahaya, ya fitar ya ce, asusun gidauniyar kai tsaye zai tafi ne wajen inganta ayyukan hukumomin tsaro, inganta samar da bayanai na sirri, tallafa wa amfani da fasaha a ɓangaren aikin tsaro, da kuma kyautata tsarin kai ɗaukin gaggawa ga al’ummomin da ke cikin buƙatar kai ɗaukin jami’an tsaro a yayin da suke cikin barazana ta tsaro.

 

Sanarwar bayan taron wanda kakakin gwamnan jihar Gombe, Ismaila Uba Misilli ya fitar, ƙungiyar ta miƙa jajenta wa mutane da gwamnatocin jihohin Kebbi, Kwara, Kogi, Neja, Sokoto, Jigawa, da Kano a bisa garkuwa da mutane da aka samu rahoton aukuwar su a cikin jihohin kwanakin baya, tare da jajanta ma waɗanda harin ‘yan ta’addan Boko Haram na baya-bayan nan ya shafa a jihohin Borno da Yobe.

 

Gwamnonin sun jinjina wa yunƙurin gaggawa da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya ɗauka wanda hakan ya kai ga samun nasarar ceto ɗaliban da aka yi garkuwa da su tare da azama da yake ƙara sanya wajen yaƙi da matsalar tsaro a faɗin ƙasar nan.

 

A yayin da suke jaddada matsayinsu da suka jima a kai, gwamnonin sun jaddada cikakken goyon bayansu ga kafa rundunar ‘yan sandan jihohi, inda suka buƙaci ‘yan majalisar tarayya da na jihohi daga yankin da su hanzarta aiwatar da duk wani da ake nema domin ganin an sami nasarar wannan batun.

 

Kungiyar ta kuma nuna damuwa kan yadda haƙo ma’adinan ba bisa ƙa’ida ba ke ƙara ta’azzara wajen haifar da rashin tsaro tare da yanke shawarar bai wa shugaba Tinubu shawarar cewa Ministan ma’adinai ya dakatar da duk wani aikin haƙar ma’adinai na tsawon watanni shida. Hakan zai ba da damar gudanar da cikakken bincike da sabunta lasisin haƙar ma’adinai tare da haɗin gwiwar gwamnatocin jihohi.

 

Gwamnonin Arewa da Sarakunan Gargajiya sun amince da muhimmancin haɗin kai, kuma ɗaukar maida hankali kan nauyin da ya rataya a wuyansu wajen tunƙarar ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

 

Sun yi alƙawarin ci gaba da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, majalisar sarauta da al’umma domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a arewa.

Arewa
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
An Yi Taron Tattaunawa Kan Littafi Na 5 Na Xi Jinping Kan Dabarun Shugabanci A Kenya

An Yi Taron Tattaunawa Kan Littafi Na 5 Na Xi Jinping Kan Dabarun Shugabanci A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.