ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Kafa Asusun Tallafa Wa Tsaro, Kowace Jiha Za Ta Riƙa Bayar Da Biliyan 1 Duk Wata

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
6 months ago
Arewa

A ƙoƙarin ƙungiyar gwamnonin Arewa na yaƙi da matsalolin tsaro da suka addabi yankin, gwamnonin sun amince da samar da Asusun Gidauniyar Tsaro na yanki da suka tsara domin samar da wadataccen kuɗaɗe don ƙarfafa ayyukan tsaro a faɗin yankin Arewa.

 

Sun cimma wannan matsayar ne a yayin zaman haɗin guiwa na musamman tsakanin ƙungiyar gwamnonin jihohin Arewan (NSGF) da Majalisar Sarakunan Arewa wanda ya gudana a Sir Kashim Ibrahim House, Kaduna ranar Litinin.

ADVERTISEMENT
  • Sultan Ya Nemi Gwamnonin Arewa Da Su Riƙa Saurarar Masu Sukarsu
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Sace A Dajin Kogi

Shugaban NSGF kuma Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya shi ne ya jagoranci zaman, wanda aka cimma matsayar cewa kowace jiha daga cikin jihohi 19 da suke faɗin Arewa za su ke bayar da gudunmawar Naira biliyan ɗaya duk wata kuma za a ke cirewa ne kai tsaye bisa tsarin da dukkanin masu ruwa da tsaki suka aminta.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Bayan cire kuɗin kai tsaye zai shiga asusun gidauniyar tsaron da aka samar domin yaƙi da matsalar tsaro ciki har da yaƙi da garkuwa da mutane.

 

Gwamnoni da sarakunan sun nuna cewa wannan matakin ya kamata a ɗauke shi tsawon lokaci domin haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen tunƙarar matsalar tsaro da ya addabi yankin tsawon shekaru.

 

A jawabin bayan taro wanda shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa Muhammadu Inuwa Yahaya, ya fitar ya ce, asusun gidauniyar kai tsaye zai tafi ne wajen inganta ayyukan hukumomin tsaro, inganta samar da bayanai na sirri, tallafa wa amfani da fasaha a ɓangaren aikin tsaro, da kuma kyautata tsarin kai ɗaukin gaggawa ga al’ummomin da ke cikin buƙatar kai ɗaukin jami’an tsaro a yayin da suke cikin barazana ta tsaro.

 

Sanarwar bayan taron wanda kakakin gwamnan jihar Gombe, Ismaila Uba Misilli ya fitar, ƙungiyar ta miƙa jajenta wa mutane da gwamnatocin jihohin Kebbi, Kwara, Kogi, Neja, Sokoto, Jigawa, da Kano a bisa garkuwa da mutane da aka samu rahoton aukuwar su a cikin jihohin kwanakin baya, tare da jajanta ma waɗanda harin ‘yan ta’addan Boko Haram na baya-bayan nan ya shafa a jihohin Borno da Yobe.

 

Gwamnonin sun jinjina wa yunƙurin gaggawa da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya ɗauka wanda hakan ya kai ga samun nasarar ceto ɗaliban da aka yi garkuwa da su tare da azama da yake ƙara sanya wajen yaƙi da matsalar tsaro a faɗin ƙasar nan.

 

A yayin da suke jaddada matsayinsu da suka jima a kai, gwamnonin sun jaddada cikakken goyon bayansu ga kafa rundunar ‘yan sandan jihohi, inda suka buƙaci ‘yan majalisar tarayya da na jihohi daga yankin da su hanzarta aiwatar da duk wani da ake nema domin ganin an sami nasarar wannan batun.

 

Kungiyar ta kuma nuna damuwa kan yadda haƙo ma’adinan ba bisa ƙa’ida ba ke ƙara ta’azzara wajen haifar da rashin tsaro tare da yanke shawarar bai wa shugaba Tinubu shawarar cewa Ministan ma’adinai ya dakatar da duk wani aikin haƙar ma’adinai na tsawon watanni shida. Hakan zai ba da damar gudanar da cikakken bincike da sabunta lasisin haƙar ma’adinai tare da haɗin gwiwar gwamnatocin jihohi.

 

Gwamnonin Arewa da Sarakunan Gargajiya sun amince da muhimmancin haɗin kai, kuma ɗaukar maida hankali kan nauyin da ya rataya a wuyansu wajen tunƙarar ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

 

Sun yi alƙawarin ci gaba da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro, majalisar sarauta da al’umma domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a arewa.

Arewa
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
An Yi Taron Tattaunawa Kan Littafi Na 5 Na Xi Jinping Kan Dabarun Shugabanci A Kenya

An Yi Taron Tattaunawa Kan Littafi Na 5 Na Xi Jinping Kan Dabarun Shugabanci A Kenya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.