ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Wasannin Motsa Jiki Na Shekarar 2024: Bambo Akani

by Leadership Hausa
2 years ago
Bambo Akani

Jaridar Leadership ta zaɓi Bambo Akani a matsayin gwazon shekara ta 2024 a fagen wasannin motsa jiki, kan ƙwazonsa na ƙarfafa guiwa da burinsa na sanya Nijeriya ta zama sahun gaba-gaba a fagen wasannin motsa jiki, da kuma samarwa matasa masu tasowa kyakkyawar makoma a fagen wasanni. Bambo Akani, wanda ya kafa kungiyar “Making of Champions Ltd (MOC)”.

Jagorancin Bambo Akani, hangen nesansa ya samar da shirin samar da gwarazan ‘yan wasa (MOC), samar da kafar watsa labarai a ɓangaren wasanni don ɗaukaka martaba da shirye-shiryen wasanni a Nijeriya, da sauran ƙasashen nahiyar Afirka, kuma ya himmatu wajen ganin ci gaban da wasanni za su kawo a Nijeriya da Afirka baki ɗaya.

  • ‘Yansanda 4,449 Sun Kai Karar Babban Sufeta Na Kasa Bisa Jinkirin Karin Girma
  • Jerin ‘Yan Wasa Uku Da Suka Zura Kwallaye 100 A Gasar Zakarun Turai

Shirinsa na samar da gwarazan ‘yan wasa, ya fara ne a shekarar 2013, tare da samar da wani taƙaitaccen tarihin wasannin motsa jiki na (Olympics) da Nijeriya ta taka a baya, kasancewar Nijeriya ƙasa ce mai albarka ɗauke da mutane masu yawa a fagen wasannin motsa jiki.

ADVERTISEMENT

Bambo Akani, ya yi imanin cewa, Nijeriya na da ƙarfin da za ta iya ƙalubalantar ƙasashe irin su Amurka da Jamaica a fagen wasannin motsa jiki, saboda akwai masu ɗimbin basira da za su sa ƙasar ta zama jigo a fagen wasanni. Yana mai cewa, “ya kamata Nijeriya ta kere Jamaica da Amurka idan har ‘yan wasan sun sa himma da gaske wajen ganin hakan ta tabbata”.

Don haka, bayan shekaru da dama ana ƙoƙarin ganin an dawo da martabar Nijeriya a fagen wasannin motsa jiki, tare da zurfin sanin Bambo Akani a fagen wasannin Olympics, a matsayinsa na haziƙin marubucin wasanni, mai daukar hoto da sanin makamar aiki, MTN ta ɗauki nauyin wani shirin wasannin a ƙarƙashin makarantar wasanni ta MOC a shekarar da ta gabata ta 2023.

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

Shirin na da manufar lalubo hanyoyin haɓaka haziƙan masu wasannin motsa jiki a ko’ina a duk faɗin Nijeriya, an bude makaranta wacce aka yi wa laƙabi da ‘Jamaican High School CHAMPS’. A cikin watan Agustan bana, an kaddamar da ajin farko na ‘yan wasa 20 na kakar wasa ta biyu na MTN CHAMPS a makarantar horas da wasannin motsa jiki ta MOC da ke Legas.

’Yan wasan da suka haɗa da maza bakwai (sprinters) da maza biyar (quarter milers) da mata biyar (sprinters) da kuma mata uku (quartermilers), an zaɓo su ne daga cikin ’yan wasan da suka yi fice a kakar wasa ta biyu na farkon gasar MTN CHAMPS da MOC ta gabatar a jihohin Akwa Ibom da Abia da Anambra da Filato da Kano da Neja da Osun da Oyo da kuma Jihar Ribas.

Matasa da dama, sun dauki wasanni a matsayin nishaɗi na ɗan wucin gadi, amma ga waɗannan gwarazan ‘yan wasa matasa 20, hanya ce ta samun kyakkyawar makoma, wannan babbar jinjina ce ga shirin MOC.

A wani ɓangare na hadin guiwar da MTN ke yi da MOC, ‘yan wasa 20 ɗinnan, za su samu damar amfani da kayayyakin motsa jiki kyauta da samun malamin horo kwararre da kuma tsarin ci gaba da samun kyakkyawar kulawa mai inganci na tsawon zamansu shekara guda a makarantar, wanda aka tsara shi don bunƙasa ƙwarewarsu don su shiga a dama da su a gasar ƙasa da ƙasa, kamar wasannin gamayyar ƙasashe rainon Birtaniya (Commonwealth) da na Olympics.

Saboda samun irin waɗannan yunƙuri wanda ba a taɓa ganin irinsa ba a Nijeriya, hakan ya sa ta zama ƙasa ɗaya daga cikin manyan ƙasashe da ke samun lambar yabo a wasannin motsa jiki ta duniya, don haka Bambo Akani ya cancanci wannan lambar yabo.

Bambo Akani
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura

MASU ALAKA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya
Labarai

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Next Post
Sojojin Ruwan Sin Da Na Kasashen Yankin Tekun Guinea Za Su Tattauna Game Da Tsaron Teku

Sojojin Ruwan Sin Da Na Kasashen Yankin Tekun Guinea Za Su Tattauna Game Da Tsaron Teku

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.