Lokacin da hasken rana na farko na shekara ta 2026 ya haskaka nahiyar Afirka, yanayin ci gaban Afirka yana bayyana a fili. Idan aka waiwayi shekara ta 2025 da ta gabata, sakamakon hadin gwiwar Sin da Afirka a fagen manyan ababen more rayuwa, ya kafa ingantaccen tushe ga taswirar ci gaban nahiyar Afirka a shekarar 2026.
A yankin hamadar Sahara, an kammala aikin shimfida layin dogo na Aljeriya wanda wani kamfanin Sin ya gina, kuma a tudun gabashin Afirka, layin dogo tsakanin Tanzania da Zambia wanda ake kira “Hanyar Abota” wanda tuni aka fara sabuntawa. Wadannan batutuwa ba kawai matakai ne na aikin gini ba, har ma sun zamo cikakkun misalan aiwatar da “Shawarar Tabbatar Da Cigaban Duniya”(GDI) da Sin ta gabatar. Yayin da har yanzu mutanen duniya ke tattaunawa kan yadda za a cike gibin ci gaban duniya, Kasar Sin da kasashen Afirka, ta hanyar shimfida layukan dogo masu inganci, suna tabbatar da ra’ayoyin da shawarar GDI ta kunsa, irin na “mayar da bukatun jama’a gaban komai”, da “daukar hakikanan matakai”. Matakin ya bullo da wata sabuwar hanyar hadin gwiwar kasashe masu tasowa, a kokarin raya ingantattun ayyuka da karfin dogaro da kai.
Shawarar GDI da Sin ta gabatar, ba magana ce mara tushe ba, kuma ka’idarta ta farko ita ce “karfafa ikon samun ci gaban kowace kasa”. Aikin sabunta layin dogo tsakanin Tanzania da Zambia ya zama misalin ka’idar. Inda bangaren Sin a wannan karo ba ma kawai ya sabunta layin da taragun ba ne, har ma ya samar da wani muhimman ci gaba, wato ba da taimako ga aikin gudanarwa da kulawa da aikin a nan gaba. Cibiyar horaswa dangane da wannan layin dogo da Sin ta kafa, da zummar horar da ma’aikata ’yan kasar Tanzaniya da Zambia, mataki ne dake bayyana cewa ba wai kawai ana gudanar da hadin gwiwa wajen baiwa wannan tsohuwar hanya ta kusan rabin karni sabon kuzari ba ne, har ma da nufin taimakawa wadannan kasashe biyu wajen samun karfin dogaro da kansu, a fannin gudanar da harkokin layin dogo, da samun riba daga jerin sana’o’i dake da nasaba da layin dogo. Wannan ya dace da bukatun shawarar GDI, wato habaka karfin samun ci gaba mai dorewa.
Hakazalika, a Aljeriya, ba kawai layin dogo da jiragen kasa aka samar ba, har ma da cikakkun ma’aunai na Sin na layin dogo da suka dace da yanayin hamada, har ma da taimaka wa bangaren Aljeriya wajen gina tsarin fasaha mai dacewa da halayen kasar. Layin dogo, a nan ya zama “dakin koyar da fasaha”, ba wai kawai hanyar jigilar kaya ko fasinjoji ba ne, wato har ma ya daga matsayin fasahohi da masana’antu na kasar.
Ban da haka, Sin ta tsara layin dogo na yammacin Aljeriya bisa ainihin bukatun kasar, duba da cewa Aljeriya tana matukar bukatar hada babban ma’adinin karfe dake cikin kasa da tashar jiragen ruwa ta Bahar Rum, ta yadda Aljeriya ke iya samun wata hanyar ci gaban masana’antar karfe, da habaka karin sana’o’i masu alaka da albarkatu.
A Gabashin Afirka, aikin layin tashar jiragen ruwa ta Lamu yana nufin baiwa kasasr Sudan ta Kudu, da Habasha damammakin ci gabansu, matakin da ya bayyana ruhin shawarar GDI a fili, wato “kar a bar wata kasa, ko wani mutum a baya”.
A hakika, salon hadin gwiwar Sin da Afirka na sauyawa daga “Abubuwan da Sin ke ginawa a Afirka”, zuwa “Karfin wasu fannoni da Sin da Afirka suke ginawa tare”. Ruhin shawarar GDI ta samar da daidaito, da daukar hakikanan matakai, da tabbatar da dorewar ci gaba, sun bayyana a fili cikin wadannan layukan dogo, da tashoshin jiragen ruwa, da tashoshin wutar lantarki, da aka gina. Wannan ba habaka kayan more rayuwa ne kadai ba, har ma misali ne na daidaitacciyar hanyar samun ci gaba: A yi hadin gwiwa wajen gina ababan more rayuwa, gami da karfafa karfin samun ci gaba ta hanyar dogaro da kai. (Mai rubuta: MINA)















Discussion about this post