ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Manyan Ababen More Rayuwa Ya Samu Babban Ci Gaba A 2025 

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Afirka

Lokacin da hasken rana na farko na shekara ta 2026 ya haskaka nahiyar Afirka, yanayin ci gaban Afirka yana bayyana a fili. Idan aka waiwayi shekara ta 2025 da ta gabata, sakamakon hadin gwiwar Sin da Afirka a fagen manyan ababen more rayuwa, ya kafa ingantaccen tushe ga taswirar ci gaban nahiyar Afirka a shekarar 2026.

A yankin hamadar Sahara, an kammala aikin shimfida layin dogo na Aljeriya wanda wani kamfanin Sin ya gina, kuma a tudun gabashin Afirka, layin dogo tsakanin Tanzania da Zambia wanda ake kira “Hanyar Abota” wanda tuni aka fara sabuntawa. Wadannan batutuwa ba kawai matakai ne na aikin gini ba, har ma sun zamo cikakkun misalan aiwatar da “Shawarar Tabbatar Da Cigaban Duniya”(GDI) da Sin ta gabatar. Yayin da har yanzu mutanen duniya ke tattaunawa kan yadda za a cike gibin ci gaban duniya, Kasar Sin da kasashen Afirka, ta hanyar shimfida layukan dogo masu inganci, suna tabbatar da ra’ayoyin da shawarar GDI ta kunsa, irin na “mayar da bukatun jama’a gaban komai”, da “daukar hakikanan matakai”. Matakin ya bullo da wata sabuwar hanyar hadin gwiwar kasashe masu tasowa, a kokarin raya ingantattun ayyuka da karfin dogaro da kai.

Shawarar GDI da Sin ta gabatar, ba magana ce mara tushe ba, kuma ka’idarta ta farko ita ce “karfafa ikon samun ci gaban kowace kasa”. Aikin sabunta layin dogo tsakanin Tanzania da Zambia ya zama misalin ka’idar. Inda bangaren Sin a wannan karo ba ma kawai ya sabunta layin da taragun ba ne, har ma ya samar da wani muhimman ci gaba, wato ba da taimako ga aikin gudanarwa da kulawa da aikin a nan gaba. Cibiyar horaswa dangane da wannan layin dogo da Sin ta kafa, da zummar horar da ma’aikata ’yan kasar Tanzaniya da Zambia, mataki ne dake bayyana cewa ba wai kawai ana gudanar da hadin gwiwa wajen baiwa wannan tsohuwar hanya ta kusan rabin karni sabon kuzari ba ne, har ma da nufin taimakawa wadannan kasashe biyu wajen samun karfin dogaro da kansu, a fannin gudanar da harkokin layin dogo, da samun riba daga jerin sana’o’i dake da nasaba da layin dogo. Wannan ya dace da bukatun shawarar GDI, wato habaka karfin samun ci gaba mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, a Aljeriya, ba kawai layin dogo da jiragen kasa aka samar ba, har ma da cikakkun ma’aunai na Sin na layin dogo da suka dace da yanayin hamada, har ma da taimaka wa bangaren Aljeriya wajen gina tsarin fasaha mai dacewa da halayen kasar. Layin dogo, a nan ya zama “dakin koyar da fasaha”, ba wai kawai hanyar jigilar kaya ko fasinjoji ba ne, wato har ma ya daga matsayin fasahohi da masana’antu na kasar.

Ban da haka, Sin ta tsara layin dogo na yammacin Aljeriya bisa ainihin bukatun kasar, duba da cewa Aljeriya tana matukar bukatar hada babban ma’adinin karfe dake cikin kasa da tashar jiragen ruwa ta Bahar Rum, ta yadda Aljeriya ke iya samun wata hanyar ci gaban masana’antar karfe, da habaka karin sana’o’i masu alaka da albarkatu.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

A Gabashin Afirka, aikin layin tashar jiragen ruwa ta Lamu yana nufin baiwa kasasr Sudan ta Kudu, da Habasha damammakin ci gabansu, matakin da ya bayyana ruhin shawarar GDI a fili, wato “kar a bar wata kasa, ko wani mutum a baya”.

A hakika, salon hadin gwiwar Sin da Afirka na sauyawa daga “Abubuwan da Sin ke ginawa a Afirka”, zuwa “Karfin wasu fannoni da Sin da Afirka suke ginawa tare”. Ruhin shawarar GDI ta samar da daidaito, da daukar hakikanan matakai, da tabbatar da dorewar ci gaba, sun bayyana a fili cikin wadannan layukan dogo, da tashoshin jiragen ruwa, da tashoshin wutar lantarki, da aka gina. Wannan ba habaka kayan more rayuwa ne kadai ba, har ma misali ne na daidaitacciyar hanyar samun ci gaba: A yi hadin gwiwa wajen gina ababan more rayuwa, gami da karfafa karfin samun ci gaba ta hanyar dogaro da kai. (Mai rubuta: MINA)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Manyan ‘Yan Siyasar Nijeriya Da Taurarunsu Za Su Haska A 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.