An samu cece-kuce a shekarar 2024 da ta girgiza gwamnati, wadda ta kai ga dakatarwa da korar ministan harkokin jinƙai, Betta Edu, da shugabar hukumar kula da shirye-shiryen harkoki jinƙai ta ƙasa (NSIPA), Halima Shehu, ya dawo da wasu labarai.
Edu da Shehu sun yi musayar zarge-zarge na karkatar da dubban biliyoyin naira na kuɗaɗen gwamnati zuwa asusun ƙashin kai, wanda hakan ya sa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa (EFCC) ta fara bincike. Rahotanni sun nuna cewa hukumar ta samu kusan naira biliyan 30 daga asusu 50 daban-daban.
Gwamnati ta sallami dukkansu daga muƙamansu ba tare da bayyana laifi da suka yi a fili ba. Shehu na ganin kamar akwai wani tsarin da ba a rubuta ba, kuma tana ganin wannan hanyar ta zo mata da hasara.
A cikin kiran da aka wallafa a kafafen sada zumunta da sauran manhajoji, tsohuwar shugabar hukumar NSIPA ta yi kira ga Shugaban ƙasa, Bola Tinubu da ya fitar da sakamakon binciken EFCC, tana jayayya cewa sunanta ya sami lahani ba tare da adalci ba.
Ta kuma bayar da goyon bayanta na siyasa ga Tinubu kafin zaɓen 2023, kuma ta ce ta shigar da koke ga shugabancin ƙasa da sakataren gwamnatin tarayya da hukuar EFCC, tana neman a fitar da rahoton binciken ga jama’a.














