Sashen kula da samar da abinci na majalisar dinkin duniya (FAO) ya bayyana cewa, fannin aikin noma na kasar nan, zai ci gaba da bayar da gudunmawarsa a bangaren saita tattalin arzikin kasar, idan har aka yi amfani da sauye-sauye a fannin, yadda ya kamata, musamman ta hanyar zuba dimbin kudade a fannin.
Wakilin sashen da kuma cibiyar ECOWAS a kasar nan, Hussein Gadain ne ya bayyana haka a wani taro a Jihar Legas.
Gadain ya yi nuni da cewa, fannin samar da abinci na kasar nan, shi ne a kan gaba tare da kuma kara bunkasa kasar.
Ya yi gargadi da cewa, rashin samar da ingantaccen tsarin samar da abinci a kasar, na iya jawo hauhawar farashin kayan abinci tare da kuma haifar da talauci.
Ya ci gaba da cewa, matsalar sauyin yanayi da kalubalen rashin tsaro, musamman a yankunan da ake yin noma da tsadar yin aikin noma a kasar nan, na haifar wa da fannin koma baya.
Sai dai, ya ce; duk da wadannan matsalolin da ya zayyano, Nijeriya na ci gaba da samun ci gaba a fannin aikin noma a kasar.
Ya ci gaba da cewa, fannin aikin noma na kasar nan, na bayar da gudunmawar da ta kai kimanin kashi 23 a cikin dari ga fannin tattalin arzikin kasar tare da kuma ciyar da ‘yan kasar sama da kashi 70 a cikin dari.
Haka zalika, ya kuma jaddada muhimmancin rage asarar da manoman kasar ke yi, idan sun yi girbi, inda ya bayar da shawarar da samar musu da kyakkyawan tsarin adana amfanin gonar da suka girbe.















Discussion about this post