Jam’iyyar NDC ta ce har yanzu ba ta fitar da ɗan takarar gwamna a Jihar Kaduna ba domin zaɓen 2027, duk da ikirarin da tsohon Sanata Danjuma La’ah da Lauya Mohammed Abbas ke yi kan kujerar. Shugaban jam’iyyar na Jihar Kaduna, Evangelist Mordecai Ibrahim, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya ce har yanzu ba a warware takaddamar tikitin jam’iyyar ba.
Ibrahim ya ce shi ne ɗan takarar gwamnan jam’iyyar da aka amince da shi a baya, kafin ya janye daga takarar da kansa. Ya ce ya sanar da Shugaban NDC na ƙasa da Kwamishinan Zaɓe na Jihar Kaduna na INEC game da janyewarsa ta hanyar wasiƙar da ya gabatar a ranar 7 ga Agusta, tare da rantsuwar tabbatar da janyewar. Ya ƙara da cewa takardar INEC da ke ɗauke da jerin sunayen ‘yan takarar jam’iyyun siyasa ta nuna sunansa a matsayin ɗan takarar NDC na gwamnan Kaduna.
Shugaban jam’iyyar ya ce bayan janyewarsa, jam’iyyar na bukatar gudanar da zaɓen fidda gwani na maye gurbi (substitution primary) domin samar da ɗan takara da doka ta amince da shi. Ya ce ikirarin da La’ah da Abbas ke yi ba zai iya warware matsalar ba, yana mai cewa: “Gaskiyar magana ita ce, a matakin jiha da na ƙasa, ba a yanke shawarar wanda zai zama ɗan takarar gwamnan Kaduna ba, ko Barrister Mohammed Sani Abbas ko Sanata Danjuma Tellah La’ah.”
Ibrahim ya kuma yi watsi da ikirarin Abbas na cewa ya halarci zaɓen fidda gwani kuma ya yi nasara, yana mai cewa hakan ba gaskiya ba ne. Ya ce bisa tanadin sashi na 31 na Dokar Zaɓe ta 2026, NDC ba ta da wani zaɓi illa gudanar da sabon zaɓen fidda gwani na maye gurbi tun da ba a cimma matsaya tsakanin masu ruwa da tsaki ba. Ya kuma bayyana cewa wasu ‘yan takarar gwamna biyu, Zariyi Madaki da Ibrahim Abdulkarim, sun janye daga takarar domin goyon bayan La’ah a taron cimma matsaya na farko da aka gudanar a shalkwatar jam’iyyar ta ƙasa.
Takaddamar ta ƙara rura wutar rikicin cikin gida na NDC a Kaduna, yayin da bangarorin jam’iyyar ke ci gaba da fafutukar samun tikitin 2027. Mataimakin Shugaban NDC na Ƙasa na Arewa, Alhaji Sidi Bomi, ya kuma yi watsi da wata takarda da ke yawo a kafafen sada zumunta mai ɗauke da sunan La’ah, yana mai cewa ba ta fito daga jam’iyyar ba. Abubuwan da suka faru na nuna cewa har yanzu NDC na buƙatar kammala tsarin cikin gida kafin ta samu ɗan takarar gwamna da za a amince da shi a hukumance.














