ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Neman Zuba Jarin Dala Biliyan 12 Daga Tsarin Tattalin Arziƙin Halal

by Abubakar Sulaiman
2 weeks ago
Halal

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da sabon shirin da ke da nufin jawo dala biliyan 12 na zuba jari daga kasuwar tattalin arziƙin halal ta duniya da darajarta ta kai kusan dala tiriliyan 7. Gwamnatin ta ce tana son Nijeriya ta zama ɗaya daga cikin manyan ƙasashen da ke samar da kayayyaki da ayyukan halal, tare da ƙirƙirar ayyukan yi da ƙara fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ne ya bayyana hakan a Legas yayin taron Lagos Halal Leadership Reception 2026, inda ƙaramin Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Dakta Doris Uzoka-Anite, ta wakilce shi. Ya ce Nijeriya ba za ta iya ci gaba da kasancewa mai sayen kayayyakin halal kawai ba yayin da wasu ƙasashe ke cin moriyar mafi yawan kuɗaɗen da ake samu daga wannan babbar kasuwa ba.

Shettima ya ce tattalin arziƙin halal ya wuce harkar abinci da abin sha, domin yanzu ya haɗa da kuɗaɗen Musulunci, da magunguna, da kayan kwalliya, da fannin yawon buɗe ido, da sufuri, da masana’antu da kasuwancin dijital.

ADVERTISEMENT

Ya ce yawan al’ummar Nijeriya, da albarkatun noma da kiwo, da ƙarfin ‘yan kasuwa da kuma matsayinta a Afirka na ba ta damar samun babban kaso daga kasuwar. Ya bayyana cewa Kwamitin Aiwatar da Dabarun Tattalin Arziƙin Halal na Nijeriya da aka ƙaddamar a ranar 3 ga Maris, 2026, ya tsara wasu rukuni 13 na aiwatar da shirin tare da burin tara sama da dala biliyan 12 na zuba jari.

Gwamnatin ta kuma ce tana tattaunawa da Islamic Development Bank, BADEA, D8 Halal Forum da sauran ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa domin ƙarfafa shirin. Jihohin Osun, Katsina da Kano sun kuma nuna sha’awar aiwatar da dabarun a matakin jiha, yayin da ake shirin miƙa Tsarin Gudanarwa, Alamar Halal ta Ƙasa da dandalin tantancewa da tabbatar da halal ga Majalisar Zartarwa ta Tarayya domin amincewa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sai dai Shettima ya jaddada cewa manufofi da yarjejeniyoyi kaɗai ba za su isa ba idan ba su haifar da kasuwanci, da zuba jari, ko fitar da kayayyaki da ayyukan yi ba. Ya buƙaci masana’antu, da bankuna, da fannoni masu sufuri, da manoma da ‘yan kasuwar yawon buɗe ido da fasaha su ɗauki takardar shaidar halal da tsarin bin diddigi a matsayin hanyar shiga kasuwannin duniya, yayin da NACCIMA da sauran masu ruwa da tsaki suka buƙaci Nijeriya ta daina tsaya wa kan tattaunawa kawai, ta koma aiwatar da manufofin da za su bunƙasa sarrafa albarkatun ƙasa da kuma ƙara darajar kayayyakin da ake samarwa a cikin gida.

Halal
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Firaministan Kasar Sin Ya Isa Yankin Da Zaftarewar Laka Ta Shafa A Yankin Xizang

Firaministan Kasar Sin Ya Isa Yankin Da Zaftarewar Laka Ta Shafa A Yankin Xizang

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.