ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
4 days ago
Kalaman

Assalamu alaikum wa rahmtullahi ta’ala wa barkatuh. ‘Yan uwa masu karatu da ke biye da mu a wannan shafi mai albarka ina muku barka da Juma’atu babbar rana. Mako biyu da suka gabata, darasinmu yana magana ne a kan fasaha da balagar harshen Manzon Allah (SAW).

To, a wannan makon za mu dora da darasi a kan hikimomin kalaman Manzon Allah (SAW).

Hakika an tattaro daga kalmominsa (SAW) wanda babu wani kafin shi da ya taba fada na hikimomi a cikin duk kabilun Larabawa da wadanda ba su ba, shi ya fara fadar su. Babu wani daya daga cikin masu Hikima da za a auna shi da Annabi (SAW).

ADVERTISEMENT

Yana daga cikin Hikimomin da shi ya fara fadarsu:

Hamiyar wadisu – Tanderu sun yi zafi; Annabi (SAW) ya fada wannan a ranar yakin Hunaini, yaki ya yi yaki, Sahabbai ba dama su gudu su bar Addininsu da Annabinsu, ta bangaren Kafirai su ma sun fito da duk rayuwarsu ba dama su gudu su bar iyalansu, kowa babu damar gudu, yaki ya yi yaki, da Annabi (SAW) yaga irin yadda idon kowa ya rufe ana ta gwabza yaki sai ya ce “Hamiyar wadisu – Tanderu sun yi zafi”.

LABARAI MASU NASABA

Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

Mata Hatfa Anfihi – Ya mutu dolensa; Ma’ana ya mutu a gida ko mutuwa irin wacce take zuwa ba tare da ana tsammaninta ba, ko a ce ya mutu cikin lafiya. Larabawa a Jahiliyya da farkon Musulunci ba su so su mutu a gida, an fahimci hakan ne a fadin Sayyidina Umar ga Usman bin Maz’unu yayin da yake cewa “Ina ganin girman Usman bin Maz’unu sai da na ga ya mutu ba a wurin yaki ba, sai na ce ashe ma ba wani ba ne, har sai da na ga Annabi (SAW) Ya Mutu a gida sai na fahimci cewa mutuwar gida ba ita ke nuni da ragwanta ba”. Usman bin Maz’unu Bakuraishe ne, Sufi mai yawan Ibada, shi ne wanda da ya mutu Annabi (SAW) ya yi shaida a kabarinsa yana cewa na yi shaida ne sabida in ‘yan gidana sun mutu in bizne su kusa da shi.

La yuldagul Mumin fi Hujrin Marrataini – Ba a sarar Mumini a cikin rami daya sau biyu; Ma’ana shi Mumini mai takatsantsan ne, idan ya shiga wani lamari ya ga abin bai yi kyau ba, ba zai kara shiga ba. In kuma ya kara shiga lamarin ya sake afkuwa to ya zama wawa.

Assa’idu man wu‘iza bigairihi – Mai arziki shi ne wanda ya gargadu da abin da ya samu waninsa; Ma’ana wanda yaga wani abu ya samu dan uwansa na daga bala’i to ya kamata shi ma ya san abin da dan uwansa ya aikata hakan ta faru da shi, shi ma sai ya kiyaye kafin abin shi ma ya zo kansa.

Irin wadannan suna da yawa wanda mai karatu ba zai iya tattare su ba. Abin da mai duba zai riska su ne mamakai cikin abin da ta tattare su kuma hankali ya tattare ta na daga karshenta.

Sahabbansa sun ce da shi (Annabi Muhammad SAW) Ya Rasulullahi ba mu ga wanda ya fi ka fasaha ba, sai Annabi ya ce “Me zai hana in zama na fi kowa fasaha? Da halshena aka saukar da Alkur’ani” Ma’ana Alkur’ani yarena ne. In Bahaushe bai yi Hikima cikin Larabci ba, ba komai duk da cewa Hausawan suna shiga cikin yaren su koya har su fi ‘yan yaren kwarewa. Kusan duk masu Hadisai kyawawa guda shida ba Larabawa ba ne amma sun kware, Larabci yaren duk Musulmi ne.

Alhamdulillah, yanzu duk wannan karatun da ‘yan Nijeriya suke yi na boko, da (a ce) da yarensu ake karantarwa, da yanzu sun fara kirkire-kirkire, amma dole sai sun fara iya yaren kafin su fara neman sanin ilimin Karatun.

Sannan kuma Annabi (SAW) ya sake fada a wani lokaci “Ana afsahul Arabi, baida anni min Kuraishin, wa nasha’atu fi bani Sa’adin – Ni ne mafi fasahar Larabawa, sai dai ni dan Kuraishawa ne, kuma na tashi a cikin Bani Sa’adin” wannan nau’in maganar yana nufin karfafa yabo ta hanyar nau’in zargi.

Kamar misalin yabon wani malami ga Shehu Ibrahim Kaulaha yake cewa “Shehu Ibrahim, mutum ne mai kyauta, sai dai duk yawan abin da ya ba ka sai ya raina shi (wato shi Shehu ne zai rana abin ba wanda aka ba, ba.”

Don sabida kwadayin ‘ya’yansu su koyi fasaha, Larabawan Birni suke bawa Larabawan Kauye ‘ya’yansu su taso a kauye.

Annabi (SAW) sabida Bakuraishe ne kuma ya taso a bani Sa’adu a kauye sai aka tara masa karfin bara’uwar kauye. Yanzu mutumin kauye da ka fada masa Magana, zai dawo maka da wacce ta fi taka, har ka ji mutum yana cewa ko dai dama yana jira na ne in yi masa magana. Suna da karin magana da bakar magana.

Kuma An hada masa da gogewar lafazin birni da adon maganganun ‘yan birni sannan kuma ka hada da cewa Annabin Allah ne wanda madadinsa ke zuwa daga Allah, wanda Dan’adam bai iya kewayewa da iliminsa.

Ummu Ma’abadin ta fada cikin yadda ta siffanta Annabi (SAW) cewa Maganarsa tana da dadi, a rarrabe yake yin magana, ba magana ‘yar kadan wacce ba ta biya bukata ba kuma ba azarbabi ba (surutu, ba tsayawa, ba ma’ana), kai ka ce maganarsa tsakiya ce da aka tsara, don haka aka rubuta maganarsa a matsayin Hadisi, Manzon Allah (SAW) ya kasance mai gwarjin murya amma mai dadin murya.

Yanzu kuma bari mu juya akalar darasin namu zuwa abin da ya shafi daukakar Danganensa da girman garinsa da wajen tasowarsa mai girma (SAW).

Kalaman
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ postsBio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Ganin Girma Da Kwarjinin Annabi (SAW)
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Yadda Ubangiji Ya Bai Wa Ɗan’adam Cikakken Ƴanci

MASU ALAKA

Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani
Dausayin Musulunci

Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani

August 28, 2026
Kalaman
Dausayin Musulunci

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

August 21, 2026
Kalaman
Dausayin Musulunci

Ganin Girma Da Kwarjinin Annabi (SAW)

August 14, 2026
Next Post
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026
Xi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

Xi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.