Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, ta cika hannu da wasu mata shida da maza uku bisa zargin shirya wani taron biki da suka yi wa taken “Bankwans Da Shaidan” kafin lokacin azumin Ramadan.
Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Hisbah, Dr. Mujahid Aminuddeen, ne ya bayyana haka ga ‘yan jarida a jihar, inda ya ce waɗanda ake zargi da shirya bikin a ƙarshen mako tare da gayyatar wasu mawaka da aikata ayyukan rashin ɗa’a don su yi wasanni a wajen taron, wanda suka ce an shirya shi ne domin yin bankwana da shaidan kafin fara azumin watan Ramadan a ranar 18 ga Fabrairu, 2026.
- Hukumar Hisbah Ta Kano Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama Da 12,000 A Shekarar 2025
- Hisbah Ta Lalata Barasar Da Ta Ƙwato A Katsina
Ya bayyana cewa wannan aikin ashshan ya saɓa wa ƙa’idojin ɗabi’a da dokokin jihar Kano, yana mai tabbatar da cewa za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike domin su girbi abin da suka shuka.
Har ila yau, ya yi kira ga al’umma da su kasance masu lura da tare da sanar da hukumomi duk wani abu da ya saɓawa ɗabi’a ko doka.















Discussion about this post