Gwamnatin Tarayya ta shigar da ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, bisa zargin kutse da satar bayanan waya ba bisa ƙa’ida ba. An shigar da ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CR/99/2026 da sunan Tarayyar Nijeriya a matsayin mai ƙara, yayin da El-Rufai ke matsayin wanda ake tuhuma shi kaɗai.
A takardun kotu, ana zargin cewa a ranar 13 ga Fabrairu, 2026, yayin wata hira a shirin Prime Time na Arise TV a Abuja, El-Rufai ya amince cewa shi da wasu sun sa ido tare da katsalandan a wayar Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu. Gwamnati ta ce wannan ya saɓa wa sashi na 12(1) na Dokar Laifukan Yanar Gizo (Gyara) ta 2024.
- Fadar Shugaban Ƙasa Ta Nemi A Binciki El-Rufai Kan Zargin Yin Kutse A Wayar Ribadu
- Ribadu Ya Gana da Sakataren Yaƙin Amurka Kan Iƙirarin Kashe Kiristoci A Nijeriya
Haka kuma, ana tuhumarsa da sanin mutanen da suka aikata laifin amma bai kai rahoto ga hukumomin tsaro ba, wanda ake zargin ya saɓa wa sashi na 27(b) na dokar. A wani ƙarin tuhuma, gwamnati ta ce shi da wasu da har yanzu ba a kama ba sun yi amfani da na’urorin fasaha domin satar bayanan sadarwar mai ba wa shugaban ƙasa shawara an harkokin tsaro (NSA), lamarin da ake zargin ya saɓa wa sashi na 131(2) na dokar sadarwa ta ƙasa (Nigerian Communications Act).
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a sanya ranar gurfanar da El-Rufai a gaban kotu ba.















Discussion about this post