• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Huawei Zai Tallafa Wa Ci Gaban Fasahar Nijeriya Ta Hanyar Zuba Dala Miliyan 15 Duk Shekara

by Khalid Idris Doya
12 months ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Huawei Zai Tallafa Wa Ci Gaban Fasahar Nijeriya Ta Hanyar Zuba Dala Miliyan 15 Duk Shekara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Huawei Technologies ya sha alwashin bunkasa cigaban fasahar zamani, duk da cewa ta sanar da shirinta na karfafa guiwar abokan hulda ta hanyar zuba hannun jarin dala miliyan 15 a kowace shekara.

Wannan wani mataki ne na dabarbarun Huawei wajen ganin ta habaka dangantarta da abokan hulda, don bai wa kwastomomi damar samun kima mai daraja ta hanyar sauyin da fasahar zamani ya kawo wa duniya.

A yayin taron Huawei Nigeria Connect 2024, da ya gudana a karshen mako a Legas, wanda ya hada fuskokin abokan jere wajen ganin sun tattauna hanyoyin da suka jibinci cin gajiyar fasahar sadarwar zamani (ICT), cigaban masana’antu, da sabbin dabarun cigaban kamfanoni wajen ganin an kyautata cinikayya.

Manajan gudanarwa na rukunin kasuwanci na Huawei Nigeria, Terrens Wu, ya nuna godiya da irin goyan baya da suke samu daga wajen kwastomominsu masu daraja da abokan hulda wajen isar da fasahohin zamani lungu da sako.

A cewar Wu, fasaha ta bayar da dama ga abubuwa da daman gaske, kuma, “Muna rungumar sabbin fasahohi da suka hada har da fasahar kwakwalwa da fasahar zamani a Nijeriya.”

“Yanzu haka, kowa da kowace kungiya da kuma kowace kasa kowa na magana kan tattalin arzikin fasahar zamani, musamman ganin yadda fasaha ke cigaba, cikin sauki za mu samu hanyoyin habaka tattalin arzikin fasahar zamani.

Ya ninka sau biyu na kayan da kasashe ke fitarwa (GDP) a wasu kasashe da dama.

“Don haka ina gaya mana muddin kamfani da kasashe za su rungumi sauyin fasahar zamani kuma su yi amfani da shi, tattalin arziki cikin sauki zai karu za a samu bunkasar abubuwan da kasashen ke fitarwa (GDP).”

Wu ya lura da cigaban da ma’aikatu da rassan gwamnati ke samu a Nijeriya musamman ma’aikatar kirkire-kirkiren sadarwa da tattalin arzikin zamani, kamar yadda kasar ke da burin kawar da iskar carbon a nan da zuwa 2050, lamarin da ke da bukatar muhimman maida hankali da gudunmawa.

Ya sanar da cewa, Huawei, “Akwai rukunin sola guda 100 na Huawei a Nijeriya da ke da karfin sama da MW 30.

“Domin cimma sauyin fasahar zamani, komai ya tafi yadda ya dace, mun karfafa manyan kasuwancinmu guda 6 domin bunkasa karfinmu da hidimar masana’antu daban-daban. Ba kawai zallar wannan ba, zuwa yanzu, muna da hannu sosai a harkar sadarwa, harkar sadarwa ta wayar salulu na 4G wanda ta kai kashi 84 cikin 100 a Nijeriya. A bangaren kirkirarriyar fasaha ta (AI), kashi 40 na masa’antu sun rungumi ayyukan Huawei wanda ke nuni da cewa ayyukan na tasiri da fa’ida sosai a duniyar fasahar zamani.”

Ya yi fatan cewa, abokan jerensu za su hada karfi da karfe da Huawei wajen ganin dabarbatun da suke da sun kai ga taimakon kasashe da daman gaske wajen cimma nasara a bangaren sauyin fasaha, “Muna ganin yadda ake zuba hannun jari kuma hakan ke cigaba da wakana a bangaren fahar zamani da cigaban kwakwala.”

Ya nanata cewa za su cigaba za su cigaba da duba hanyoyin taimaka wa cigaban fasahar Nijeriya da kyautata alakarsu da yayi kyau na tsawon shekara 25.

A cewarsa, a tsakanin 2018 zuwa 2023, Huawei ta horas da ‘yan Nijeriya sama da 50,000 a bangaren ICT, da wasu kamfanonin Nijeriya sama da 200 da suka samu shaidar hulda da Huawei. Ya ce, Huawei ya kuma gina cibiyoyin gudanar da ayyuka na shiyya guda 10 (RNOC) a Nijeriya da ke kula da kasashe 12 da suka hada da Nijeriya Botswana, Ghana, Sierra Leone, South Africa, Comoros, Mauritius, Tanzania, Zambia, and Somalia.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaHuaweiNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabannin Bankuna Sun Ci Bashin Naira Biliyan 549  Cikin Shekara 5

Next Post

2027: PDP Za Ta Yanke Hukunci Kan Makomata — Atiku

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

4 weeks ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

2 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

2 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

3 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

7 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

7 months ago
Next Post
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

2027: PDP Za Ta Yanke Hukunci Kan Makomata — Atiku

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.