ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Huawei Zai Tallafa Wa Ci Gaban Fasahar Nijeriya Ta Hanyar Zuba Dala Miliyan 15 Duk Shekara

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Huawei

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Huawei Technologies ya sha alwashin bunkasa cigaban fasahar zamani, duk da cewa ta sanar da shirinta na karfafa guiwar abokan hulda ta hanyar zuba hannun jarin dala miliyan 15 a kowace shekara.

Wannan wani mataki ne na dabarbarun Huawei wajen ganin ta habaka dangantarta da abokan hulda, don bai wa kwastomomi damar samun kima mai daraja ta hanyar sauyin da fasahar zamani ya kawo wa duniya.

A yayin taron Huawei Nigeria Connect 2024, da ya gudana a karshen mako a Legas, wanda ya hada fuskokin abokan jere wajen ganin sun tattauna hanyoyin da suka jibinci cin gajiyar fasahar sadarwar zamani (ICT), cigaban masana’antu, da sabbin dabarun cigaban kamfanoni wajen ganin an kyautata cinikayya.

Manajan gudanarwa na rukunin kasuwanci na Huawei Nigeria, Terrens Wu, ya nuna godiya da irin goyan baya da suke samu daga wajen kwastomominsu masu daraja da abokan hulda wajen isar da fasahohin zamani lungu da sako.

A cewar Wu, fasaha ta bayar da dama ga abubuwa da daman gaske, kuma, “Muna rungumar sabbin fasahohi da suka hada har da fasahar kwakwalwa da fasahar zamani a Nijeriya.”

“Yanzu haka, kowa da kowace kungiya da kuma kowace kasa kowa na magana kan tattalin arzikin fasahar zamani, musamman ganin yadda fasaha ke cigaba, cikin sauki za mu samu hanyoyin habaka tattalin arzikin fasahar zamani.

Ya ninka sau biyu na kayan da kasashe ke fitarwa (GDP) a wasu kasashe da dama.

“Don haka ina gaya mana muddin kamfani da kasashe za su rungumi sauyin fasahar zamani kuma su yi amfani da shi, tattalin arziki cikin sauki zai karu za a samu bunkasar abubuwan da kasashen ke fitarwa (GDP).”

Wu ya lura da cigaban da ma’aikatu da rassan gwamnati ke samu a Nijeriya musamman ma’aikatar kirkire-kirkiren sadarwa da tattalin arzikin zamani, kamar yadda kasar ke da burin kawar da iskar carbon a nan da zuwa 2050, lamarin da ke da bukatar muhimman maida hankali da gudunmawa.

Ya sanar da cewa, Huawei, “Akwai rukunin sola guda 100 na Huawei a Nijeriya da ke da karfin sama da MW 30.

“Domin cimma sauyin fasahar zamani, komai ya tafi yadda ya dace, mun karfafa manyan kasuwancinmu guda 6 domin bunkasa karfinmu da hidimar masana’antu daban-daban. Ba kawai zallar wannan ba, zuwa yanzu, muna da hannu sosai a harkar sadarwa, harkar sadarwa ta wayar salulu na 4G wanda ta kai kashi 84 cikin 100 a Nijeriya. A bangaren kirkirarriyar fasaha ta (AI), kashi 40 na masa’antu sun rungumi ayyukan Huawei wanda ke nuni da cewa ayyukan na tasiri da fa’ida sosai a duniyar fasahar zamani.”

Ya yi fatan cewa, abokan jerensu za su hada karfi da karfe da Huawei wajen ganin dabarbatun da suke da sun kai ga taimakon kasashe da daman gaske wajen cimma nasara a bangaren sauyin fasaha, “Muna ganin yadda ake zuba hannun jari kuma hakan ke cigaba da wakana a bangaren fahar zamani da cigaban kwakwala.”

Ya nanata cewa za su cigaba za su cigaba da duba hanyoyin taimaka wa cigaban fasahar Nijeriya da kyautata alakarsu da yayi kyau na tsawon shekara 25.

A cewarsa, a tsakanin 2018 zuwa 2023, Huawei ta horas da ‘yan Nijeriya sama da 50,000 a bangaren ICT, da wasu kamfanonin Nijeriya sama da 200 da suka samu shaidar hulda da Huawei. Ya ce, Huawei ya kuma gina cibiyoyin gudanar da ayyuka na shiyya guda 10 (RNOC) a Nijeriya da ke kula da kasashe 12 da suka hada da Nijeriya Botswana, Ghana, Sierra Leone, South Africa, Comoros, Mauritius, Tanzania, Zambia, and Somalia.

Huawei
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

2027: PDP Za Ta Yanke Hukunci Kan Makomata — Atiku

LABARAI MASU NASABA

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026
Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

September 14, 2026
Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

September 14, 2026
Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

September 14, 2026
Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

September 14, 2026
Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa

Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa

September 14, 2026
Huawei

Babu Dalilin Da Zai Sa Nijeriya Yin Talauci – Obasanjo

September 14, 2026
Gudummawar Da Hada-Hadar Ba Da Hidima Ta Sin Take Kawo Wa Duniya

Gudummawar Da Hada-Hadar Ba Da Hidima Ta Sin Take Kawo Wa Duniya

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.