Hukumar Kula da Babban Tarayya Abuja ta aiwatar da haramcin amfani da tsofaffin tayoyi wajen gasa sassan dabba a wajen mahauta na Kubwa, da ke Karamar Hukumar Bwari, bayan wani rahoto ya nuna irin hadarin lafiyar da wannan dabi’a ke haifarwa.
Bayan wani bincike da aka gudanar, an gano cewa wasu mahauta na amfani da tayoyi da aka kone wajen cire gashin dabbobi, lamarin da ke haifar da damuwa kan lafiyar jama’a da kuma ingancin abinci.
A ziyarar da aka sake kaiwa wurin, an ga cewa mahautan sun daina amfani da tayoyi, inda suka koma amfani da itacen wuta. An kuma ga manyan tarin itace a wuraren gasshin domin ci gaba da aikinsu.
Wasu daga cikin mahautan sun bayyana cewa jami’an Sashen Aikin Gona da Raya Karkara na FCT sun kai samame bayan rahoton ya fito, sannan suka tilasta aiwatar da haramcin.
“Bayan rahoton ne suka zo suka hana mu amfani da tayoyi. Yanzu ba mu da wani zabi illa mu koma amfani da itacen wuta,” in ji daya daga cikin mahautan, yana nuna damuwa kan karin kudin aiki.
Wani likitan dabbobi da ke aiki a wurin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da cewa an aiwatar da matakin hana amfani da tayoyi. Ya ce hukumomi sun sha gargadi kafin daukar matakin tilas.
“Mun dade muna wayar da kai kan illolin lafiya, amma ba a cika bin umarni ba. Bayan rahoton, sai muka tilasta aiwatar da haramcin,” in ji shi.
Ya kuma kara da cewa an shawarci mahauta da su daidaita farashin aikinsu saboda karin kudin da amfani da hanyoyin da ba su da illa ke jawowa, yayin da ake kuma kira ga masu saye su fi mayar da hankali kan lafiya maimakon arha.
“Ya kamata mutane su fi mayar da hankali wajen sayen nama mai inganci ko da zai dan yi tsada, maimakon su jefa kansu cikin hadarin rashin lafiya,” in ji shi.















Discussion about this post