Cibiyar Bincike Kan Dabbobi ta Kasa da ke jami’ar Ahmadu Bello Zariya, a Jihar Kaduna, ta fara gudanar da aikin kyankyshe ‘yan tsakin kaji na shekara, inda ta fara gudanar da aikin ‘yan tsakin kimanin 25,000.
Manufar aikin shi ne, domin a kare masu kiwon kaji daga asarar da suka yi a fannin na kiwon da kuma kara bunkasa sana’arsu ta kiwon.
Aikin, wanda cibiyar ta fara gudanarwa a ranar 31 ga watan Maris na 2026, an fara gudanar da shi ne da ‘yan tsaki sama da 3,000.
Nau’ikan ‘yan tsakin da aka fara kyankayeshewa, sun hada da ‘Shikabrown GPS’ da kuma masu saurin girma, wato ‘broilers’.
Aikin na kyankyashe ‘yan tsakin kimanin 25,000, ya nuna cewa; ya rubanya wanda aka fara a 2025, wadanda yawansu ya kai kimanin 17,000.
A jawabinsa a yayin da yake duba aikin, Babban Mukaddashin Darakta na cibiyar, Farfesa Muhammad Rabiu Hassan, ya nuna jin dadinsa a kan ci gaban da ake samu a aikin.
Kazalika, ya yaba da goyon bayan da suke ci gaba da samu daga wurin ministan bunkasa kiwon dabbobi, Mukhtar Idi Maiha da kuma wanda suke ci gaba da samu daga wurin shugaban jamai’ar, Farfesa Adamu Ahmed.
Haka zalika, Hassan ya yaba wa ma’aikatan cibiyar, kan kokarin da suke ci gaba da yi, musamman domin a samu cin nasarar aikin.
Shi kuwa a nasa jawabin kan aikin, shugaban shirin yin kiwon kaji, Dakta Idris Abdullahi, ya sanar da cewa; cibyar ta samu dimbin nasarori a wannan aiki.















Discussion about this post