Wani matashi mai shekaru 27 ya rasa ransa a Jihar Ogun bayan rikici ya barke kan bashin N25,000 da ya rikide zuwa tashin hankali a wata mashayar giya, inda jami’an ’yansanda suka kama wanda ake zargi da hannu a lamarin.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 na dare ranar Asabar, inda rikicin ya samo asali daga zazzafar muhawara kan wani bashi da aka ce tun bara ake binsa.
- Rikicin Jos: Tinubu Ya Jinkirta Tafiyarsa Zuwa Ogun, Zai Kai Ziyara Filato
- An Kashe Mutum Ɗaya Yayin Da Masu Fasa Ƙwauri Suka Kai Hari Kan Kwastam A Ogun
A cewar ’yansanda, wanda ake zargin ya dira wajen yana neman a biya shi bashin nan take, amma ya fusata bayan bukatarsa ba ta biya ba, lamarin da ya haddasa tashin hankali.
An ce a cikin rikicin, wanda ake zargin ya fasa kwalba tare da razanar da mutanen da ke wurin, kafin daga bisani ya kai hari kan wani mai suna Oyekunle, inda ya ji masa raunuka a hannu da ciki yayin da ake ƙoƙarin hana shi shiga cikin mashayar.
An garzaya da wanda aka kai wa harin zuwa asibitin Strong Tower da ke Giwa Oke Aro, inda daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa yayin da ake kokarin ceto ransa. Kakakin ’yansandan jihar, Oluseyi Babaseyi, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an tsare wanda ake zargin, yayin da aka ajiye gawar mamacin a dakin ajiyar gawa domin yin bincike, kafin a mika shari’ar ga sashin binciken manyan laifuka na jihar domin ci gaba da bincike da yiwuwar gurfanarwa a kotu.















Discussion about this post