ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Indomie Ta Gwangwaje Mutane 80 Da Kyautar PS5, iPhone, TV, Firinji Da Kekuna A Gasar Garabasar Samun Nasara 

by Leadership Hausa
6 months ago

Kamfanin taliyar Indomie na ci gaba da faranta ran kwastomominsa ta hanyar shirin sa na Garabasar Samun Nasara (Indomie Success Promo), wani shiri ne na musamman da aka ƙirƙiro domin karrama kwastomomi masu daraja tare da samar da kyautuka da za su ke tunawa da su da sanya su farin ciki.

Shiga cikin gasar abu ne mai sauƙi. Ana buƙatar masu sha’awa da su tattara faketin ledojin Indomie guda 10 na sabon fakiti su kai su cibiyar da ake karɓa mafi kusa da su domin samun fakitin Indomie gram 70 kyauta.

  • Bankin Duniya ya Jinjina Wa Jihar Gombe Kan Magance Zaizayar Kasa
  • Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

Duk faketin ledoji 10 ana ƙirga su a matsayin maki ɗaya. Yawan ledojin Indomie da ka tattara na ƙara yawan makinka a gasar, ka ci Indomie da yawa, ka ci nasarar lashe gasar da yawa! A ƙarshen kowane wata, mutane 80 da ke kan jadawalin da suka yi nasara da maki mai rinjaye za su samu kyaututtuka masu kayatarwa. Haka kuma, ana iya bibiyar shafin Indomie.ng/arewa, domin samun karin bayani kan gasar.

ADVERTISEMENT

A wani ɓangare na gasar, Indomie ta shirya wani gagarumin taron Kasuwannin Kano da Kaduna, inda aka nishaɗantar da jama’a. Taron ya tara jama’a da ‘yan-kasuwa masu da masu sayayya inda aka nishadantu da wasanni masu kayatarwa tare da ƙarin rabon kayatattun kyautuka daga Indomie.

Babban abin da ya fi ɗaukar hankali shi ne rabon kyaututtuka kai tsaye ga wadanda suka lashe gasar, inda waɗanda suka yi nasara suka samu kyaututtuka kamar PS5 da wayoyin iPhone da firiza da mazubin gas na girki da talabijin da kuma kekuna. Wannan rabon kyaututtuka ya sanya farin ciki a zukatan mahalarta taron, tare da ƙara tabbatar da gaskiya da sahihancin gasar.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Da yake jawabi a wajen taron, Jamiu Abdulrasheed ya bayyana cewa: “Ganin farin ciki da annashuwa a fuskar kwastomominmu yana nuna mana cewa duk ƙoƙarin da muka yi wajen shirya wannan gasar ya yi tasiri. Wannan shiri hanya ce ta nuna musu godiya tare da ba su damar cin manyan kyaututtuka.”

Wasu daga cikin waɗanda suka yi nasara sun bayyana cewa nasarar ta zo musu a bazata kuma ta sanya su farin ciki matuka, tare da ƙarfafa wa sauran jama’a gwiwa da su shiga cikin gasar a dama da su suma su amfana.

Baya ga nishaɗi, taron ya taimaka wajen bunƙasa hada-hada Kasuwannin biyu, inda yawan jama’a ya ƙaru tare da hada-hadar harkokin kasuwanci a yankunan da aka gudanar da gasar.

Har yanzu akwai sauran kyaututtuka da za a ci, Indomie na ƙarfafa wa jama’a gwiwa da su ci gaba da shiga gasar tare da cin Indomie domin ƙara samun damar cin nasara a gasar.

Domin ƙarin bayani, ana shawartar jama’a da su rika bibiyar shafukan sada-zumunta na kamfanin musamman @Indomie Arewa.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Mataimakin Shugaba Sin Ya Gana Da Shugaban Afrika Ta Kudu Kan Dangantakar Kasashen Biyu 

Mataimakin Shugaba Sin Ya Gana Da Shugaban Afrika Ta Kudu Kan Dangantakar Kasashen Biyu 

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.