ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Indomie Ta Gwangwaje Mutane 80 Da Kyautar PS5, iPhone, TV, Firinji Da Kekuna A Gasar Garabasar Samun Nasara 

by Leadership Hausa
3 months ago

Kamfanin taliyar Indomie na ci gaba da faranta ran kwastomominsa ta hanyar shirin sa na Garabasar Samun Nasara (Indomie Success Promo), wani shiri ne na musamman da aka ƙirƙiro domin karrama kwastomomi masu daraja tare da samar da kyautuka da za su ke tunawa da su da sanya su farin ciki.

Shiga cikin gasar abu ne mai sauƙi. Ana buƙatar masu sha’awa da su tattara faketin ledojin Indomie guda 10 na sabon fakiti su kai su cibiyar da ake karɓa mafi kusa da su domin samun fakitin Indomie gram 70 kyauta.

  • Bankin Duniya ya Jinjina Wa Jihar Gombe Kan Magance Zaizayar Kasa
  • Yadda Takarar Obi Ta Zama Kamar Wani Wasan Barkwanci

Duk faketin ledoji 10 ana ƙirga su a matsayin maki ɗaya. Yawan ledojin Indomie da ka tattara na ƙara yawan makinka a gasar, ka ci Indomie da yawa, ka ci nasarar lashe gasar da yawa! A ƙarshen kowane wata, mutane 80 da ke kan jadawalin da suka yi nasara da maki mai rinjaye za su samu kyaututtuka masu kayatarwa. Haka kuma, ana iya bibiyar shafin Indomie.ng/arewa, domin samun karin bayani kan gasar.

ADVERTISEMENT

A wani ɓangare na gasar, Indomie ta shirya wani gagarumin taron Kasuwannin Kano da Kaduna, inda aka nishaɗantar da jama’a. Taron ya tara jama’a da ‘yan-kasuwa masu da masu sayayya inda aka nishadantu da wasanni masu kayatarwa tare da ƙarin rabon kayatattun kyautuka daga Indomie.

Babban abin da ya fi ɗaukar hankali shi ne rabon kyaututtuka kai tsaye ga wadanda suka lashe gasar, inda waɗanda suka yi nasara suka samu kyaututtuka kamar PS5 da wayoyin iPhone da firiza da mazubin gas na girki da talabijin da kuma kekuna. Wannan rabon kyaututtuka ya sanya farin ciki a zukatan mahalarta taron, tare da ƙara tabbatar da gaskiya da sahihancin gasar.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

Da yake jawabi a wajen taron, Jamiu Abdulrasheed ya bayyana cewa: “Ganin farin ciki da annashuwa a fuskar kwastomominmu yana nuna mana cewa duk ƙoƙarin da muka yi wajen shirya wannan gasar ya yi tasiri. Wannan shiri hanya ce ta nuna musu godiya tare da ba su damar cin manyan kyaututtuka.”

Wasu daga cikin waɗanda suka yi nasara sun bayyana cewa nasarar ta zo musu a bazata kuma ta sanya su farin ciki matuka, tare da ƙarfafa wa sauran jama’a gwiwa da su shiga cikin gasar a dama da su suma su amfana.

Baya ga nishaɗi, taron ya taimaka wajen bunƙasa hada-hada Kasuwannin biyu, inda yawan jama’a ya ƙaru tare da hada-hadar harkokin kasuwanci a yankunan da aka gudanar da gasar.

Har yanzu akwai sauran kyaututtuka da za a ci, Indomie na ƙarfafa wa jama’a gwiwa da su ci gaba da shiga gasar tare da cin Indomie domin ƙara samun damar cin nasara a gasar.

Domin ƙarin bayani, ana shawartar jama’a da su rika bibiyar shafukan sada-zumunta na kamfanin musamman @Indomie Arewa.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
Labarai

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe
Labarai

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Next Post
Mataimakin Shugaba Sin Ya Gana Da Shugaban Afrika Ta Kudu Kan Dangantakar Kasashen Biyu 

Mataimakin Shugaba Sin Ya Gana Da Shugaban Afrika Ta Kudu Kan Dangantakar Kasashen Biyu 

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.