ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Ya Ce Har Yanzu Bai Gamsu Da Tattaunawar Yarjejeniyar Da Ake Yi Da Iran Ba

by Sadiq
2 months ago

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce har yanzu bai gamsu da shawarwarin Iran ba a tattaunawar da ake yi kan yarjejeniyar zaman lafiya, duk da rahotannin da ke cewa an riga da cimma matsaya.

A wani taron majalisar ministoci a Fadar White House, Trump ya ce Iran na son yarjejeniyar amma har yanzu ba ta cika sharuɗan Amurka ba.

Ya kuma ce ba zai yi gaggawa wajen kammala tattaunawar ba.

ADVERTISEMENT

“Iran na matuƙar son yin yarjejeniyar, amma har yanzu ba su kai ga inda ake so ba. Ba mu gamsu ba,” in ji Trump, yana mai gargaɗin cewa Amurka na iya “kammala aiki” idan tattaunawar ta faskara.

Kafofin yaɗa labarai na Iran sun ruwaito cewa akwai daftarin yarjejeniyar da zai sassauta takunkumi da kuma buɗe muhimman hanyoyin jiragen ruwa kamar mashigar Hormuz.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Sai dai Fadar White House ta ƙaryata rahoton, tana mai cewa ƙarya ne.

Trump ya ce Amurka ba za ta amince Iran ko wata ƙasa ta mallaki ko sarrafa wannan muhimmin mashigar ruwa ba.

Ya kuma yi barazanar ɗaukar matakin soja idan ya zama dole.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ya ce an samu ɗan ci gaba a tattaunawar, amma ba a kai ga cimma matsaya ba.

Trump ya kuma danganta yarjejeniyar da sauran batutuwan diflomasiyya a Gabas ta Tsakiya, yana mai cewa yarjejeniyar na iya danganta da ƙarin ƙasashen da suka ƙulla dangantaka da Isra’ila.

Ya ce ko da yake zai iya amincewa da yarjejeniyar na wucin gadi kan batun nukiliyar Iran, ba zai yadda Rasha ko China su riƙa ajiyar uranium na Iran ba.

Tattaunawar na ci gaba a daidai lokacin da ake fuskantar tashin hankali a duniya da kuma matsin tattalin arziƙi gabanin zaɓukan Amurka masu zuwa.

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Ramadan: ‘Yansanda Sun Buƙaci A Sanya Ido A Kano A Goman Ƙarshe

'Yansanda Sun Kama Wasu Kan Zargin Ɓarnata Kayan Gwamnati Da Fashi A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

July 18, 2026
Xi Jinping Ya Bukaci A Gudanar Da Aikin Ceto A Tsanake Bayan Rugujewar Bangaren Wani Tsauni A Chongqing

Xi Jinping Ya Bukaci A Gudanar Da Aikin Ceto A Tsanake Bayan Rugujewar Bangaren Wani Tsauni A Chongqing

July 18, 2026
Yadda Ake Miyar Karkashi Da Nama

Yadda Ake Miyar Karkashi Da Nama

July 18, 2026
Kura-kurai 7 Da Mata Ke Yi Wajen Kula Da Fatarsu

Kura-kurai 7 Da Mata Ke Yi Wajen Kula Da Fatarsu

July 18, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

July 18, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.