Shugaban Amurka Donald Trump ya ce har yanzu bai gamsu da shawarwarin Iran ba a tattaunawar da ake yi kan yarjejeniyar zaman lafiya, duk da rahotannin da ke cewa an riga da cimma matsaya.
A wani taron majalisar ministoci a Fadar White House, Trump ya ce Iran na son yarjejeniyar amma har yanzu ba ta cika sharuɗan Amurka ba.
Ya kuma ce ba zai yi gaggawa wajen kammala tattaunawar ba.
“Iran na matuƙar son yin yarjejeniyar, amma har yanzu ba su kai ga inda ake so ba. Ba mu gamsu ba,” in ji Trump, yana mai gargaɗin cewa Amurka na iya “kammala aiki” idan tattaunawar ta faskara.
Kafofin yaɗa labarai na Iran sun ruwaito cewa akwai daftarin yarjejeniyar da zai sassauta takunkumi da kuma buɗe muhimman hanyoyin jiragen ruwa kamar mashigar Hormuz.
Sai dai Fadar White House ta ƙaryata rahoton, tana mai cewa ƙarya ne.
Trump ya ce Amurka ba za ta amince Iran ko wata ƙasa ta mallaki ko sarrafa wannan muhimmin mashigar ruwa ba.
Ya kuma yi barazanar ɗaukar matakin soja idan ya zama dole.
Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ya ce an samu ɗan ci gaba a tattaunawar, amma ba a kai ga cimma matsaya ba.
Trump ya kuma danganta yarjejeniyar da sauran batutuwan diflomasiyya a Gabas ta Tsakiya, yana mai cewa yarjejeniyar na iya danganta da ƙarin ƙasashen da suka ƙulla dangantaka da Isra’ila.
Ya ce ko da yake zai iya amincewa da yarjejeniyar na wucin gadi kan batun nukiliyar Iran, ba zai yadda Rasha ko China su riƙa ajiyar uranium na Iran ba.
Tattaunawar na ci gaba a daidai lokacin da ake fuskantar tashin hankali a duniya da kuma matsin tattalin arziƙi gabanin zaɓukan Amurka masu zuwa.















Discussion about this post