ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyalan Sheikh Khalifa Abdulkadir Sun Koka Kan Rashin Sanin Halin Da Yake Ciki

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
Sheikh Khalifa

Uwargida da ‘ya’yan fitaccen malamin addinin musulinci a Zariya, Sheikh Khalifa Sani Abdulkadir, sun koka kan bacewarsa kwanaki 25 bayan da ya tafi Abuja, sakamakon rufe asusun ajiyarsa na banki da aka yi.

Malamin dai, na daya daga cikin manyan jagororin kungiyar Fityanul Islam da kuma kungiyar Tijjaniyya a Zariya da fadin Jihar Kaduna baki-daya.

  • Manufar Yada-Zango Ba Tare Da Bukatar Biza Ba Ta Bunkasa Adadin Masu Shigowa Kasar Sin Domin Ziyara
  • Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Tiriliyan ₦4.4 Na Shekarar 2026

Da take magana a wata hira da RFI International da ke Kaduna, matar malamin, Hajiya Ramatu Khalifa Sani Abdulkadir ta ce; maigidan nata ya bar gida da sanyin safiya, bayan ya shaida mata cewa, zai tafi Abuja domin warware matsalolin da suka shafi asusun ajiyarsa na banki.

ADVERTISEMENT

Ta kara da cewa, “Ya buga min kofa da safe, na ce masa ina yin addu’a ne, daga nan sai ya ba ni kudin da za a yi amfani da su a gida, ya ce zai tafi Abuja, in sha Allahu zai dawo a ranar, ba zai kwana ba.

“Tun daga wannan rana, har zuwa yanzu; ban sake jin muryarsa ba, duk lokacin da na kira layinsa, a kashe, yau kwana 25 kenan ban sake jin muryarsa ba.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

“Ni kadai ce yanzu a gida tare da yara, ina cikin tashin hankali matuka, da ta kai ko barci ba na iya yi, duk da cewa dai, na kan yi kokarin yin karfin hali, don kada yaran su firgita, amma ko shakka babu, muna cikin damuwa da tashin hankali kwarai da gaske.” Ta kara da cewa, daga baya aka sanar da ‘yan’uwa cewa; ana tuhumar mijin nata a kan kudi kusan naira miliyan biyu.

Ta ce, “An ce an toshe asusun ajiyarsa, wannan dalili ne ya sa ya tafi Abuja, domin a bude masa, daga baya kuma sai aka ce mana yana da alaka da da tuhuma a kan naira miliyan biyu.

Dan malamin, Sunusi Khalifa Sani Abdulkadir, wanda ya raka mahaifin nasa, ya bayyana abin da ya faru a tafiyar tasu zuwa Abuja.

Ya bayyana cewa, “Bayan an rufe asusun nasa, sai ya nemi dalilin da ya sa aka rufe, aka ce hukumar EFCC ce, sannan kuma za a iya bude asusun ne kadai, da zarar ya je ofishin nasu.

“Bayan sun yi wa shehin tambayoyi, sai suka ce akwai kudi kimanin naira miliyan biyu da aka aike masa, don haka suna kan yin bincike a kai, suka kara da cewa, wani ya hada shi da wani mutum da yake neman addu’o’in da suka shafi rayuwarsa, kuma ya aiwatar da addu’o’in kamar yadda ya nema.”

Ya kara da cewa, daga baya hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta bayyana lamarin a matsayin wanda ya shafi harkar sojoji.

Ya kara da cewa, “Binciken yana da alaka da sojoji, tuni kuma sun sanar da su, su ma sun ce mahaifin nawa ya amince a mayar da kudin, amma sai sojojin suka ce za su zo su yi masa tambayoyi, tun daga ranar; yanzu kwana 25 kenan ba mu sake ganinsa ba.

Sheikh Khalifa
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
Sheikh Khalifa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Nijeriya

Abin Da ‘Yan Nijeriya Ke Bukata A 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.