ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyalan Sheikh Khalifa Abdulkadir Sun Koka Kan Rashin Sanin Halin Da Yake Ciki

by Sani Anwar and Sulaiman
6 months ago
Sheikh Khalifa

Uwargida da ‘ya’yan fitaccen malamin addinin musulinci a Zariya, Sheikh Khalifa Sani Abdulkadir, sun koka kan bacewarsa kwanaki 25 bayan da ya tafi Abuja, sakamakon rufe asusun ajiyarsa na banki da aka yi.

Malamin dai, na daya daga cikin manyan jagororin kungiyar Fityanul Islam da kuma kungiyar Tijjaniyya a Zariya da fadin Jihar Kaduna baki-daya.

  • Manufar Yada-Zango Ba Tare Da Bukatar Biza Ba Ta Bunkasa Adadin Masu Shigowa Kasar Sin Domin Ziyara
  • Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Tiriliyan ₦4.4 Na Shekarar 2026

Da take magana a wata hira da RFI International da ke Kaduna, matar malamin, Hajiya Ramatu Khalifa Sani Abdulkadir ta ce; maigidan nata ya bar gida da sanyin safiya, bayan ya shaida mata cewa, zai tafi Abuja domin warware matsalolin da suka shafi asusun ajiyarsa na banki.

ADVERTISEMENT

Ta kara da cewa, “Ya buga min kofa da safe, na ce masa ina yin addu’a ne, daga nan sai ya ba ni kudin da za a yi amfani da su a gida, ya ce zai tafi Abuja, in sha Allahu zai dawo a ranar, ba zai kwana ba.

“Tun daga wannan rana, har zuwa yanzu; ban sake jin muryarsa ba, duk lokacin da na kira layinsa, a kashe, yau kwana 25 kenan ban sake jin muryarsa ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

“Ni kadai ce yanzu a gida tare da yara, ina cikin tashin hankali matuka, da ta kai ko barci ba na iya yi, duk da cewa dai, na kan yi kokarin yin karfin hali, don kada yaran su firgita, amma ko shakka babu, muna cikin damuwa da tashin hankali kwarai da gaske.” Ta kara da cewa, daga baya aka sanar da ‘yan’uwa cewa; ana tuhumar mijin nata a kan kudi kusan naira miliyan biyu.

Ta ce, “An ce an toshe asusun ajiyarsa, wannan dalili ne ya sa ya tafi Abuja, domin a bude masa, daga baya kuma sai aka ce mana yana da alaka da da tuhuma a kan naira miliyan biyu.

Dan malamin, Sunusi Khalifa Sani Abdulkadir, wanda ya raka mahaifin nasa, ya bayyana abin da ya faru a tafiyar tasu zuwa Abuja.

Ya bayyana cewa, “Bayan an rufe asusun nasa, sai ya nemi dalilin da ya sa aka rufe, aka ce hukumar EFCC ce, sannan kuma za a iya bude asusun ne kadai, da zarar ya je ofishin nasu.

“Bayan sun yi wa shehin tambayoyi, sai suka ce akwai kudi kimanin naira miliyan biyu da aka aike masa, don haka suna kan yin bincike a kai, suka kara da cewa, wani ya hada shi da wani mutum da yake neman addu’o’in da suka shafi rayuwarsa, kuma ya aiwatar da addu’o’in kamar yadda ya nema.”

Ya kara da cewa, daga baya hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta bayyana lamarin a matsayin wanda ya shafi harkar sojoji.

Ya kara da cewa, “Binciken yana da alaka da sojoji, tuni kuma sun sanar da su, su ma sun ce mahaifin nawa ya amince a mayar da kudin, amma sai sojojin suka ce za su zo su yi masa tambayoyi, tun daga ranar; yanzu kwana 25 kenan ba mu sake ganinsa ba.

Sheikh Khalifa
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Sheikh Khalifa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Next Post
Nijeriya

Abin Da ‘Yan Nijeriya Ke Bukata A 2026

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.