Uwargida da ‘ya’yan fitaccen malamin addinin musulinci a Zariya, Sheikh Khalifa Sani Abdulkadir, sun koka kan bacewarsa kwanaki 25 bayan da ya tafi Abuja, sakamakon rufe asusun ajiyarsa na banki da aka yi.
Malamin dai, na daya daga cikin manyan jagororin kungiyar Fityanul Islam da kuma kungiyar Tijjaniyya a Zariya da fadin Jihar Kaduna baki-daya.
- Manufar Yada-Zango Ba Tare Da Bukatar Biza Ba Ta Bunkasa Adadin Masu Shigowa Kasar Sin Domin Ziyara
- Majalisar Dokokin Legas Ta Amince Da Kasafin Tiriliyan ₦4.4 Na Shekarar 2026
Da take magana a wata hira da RFI International da ke Kaduna, matar malamin, Hajiya Ramatu Khalifa Sani Abdulkadir ta ce; maigidan nata ya bar gida da sanyin safiya, bayan ya shaida mata cewa, zai tafi Abuja domin warware matsalolin da suka shafi asusun ajiyarsa na banki.
Ta kara da cewa, “Ya buga min kofa da safe, na ce masa ina yin addu’a ne, daga nan sai ya ba ni kudin da za a yi amfani da su a gida, ya ce zai tafi Abuja, in sha Allahu zai dawo a ranar, ba zai kwana ba.
“Tun daga wannan rana, har zuwa yanzu; ban sake jin muryarsa ba, duk lokacin da na kira layinsa, a kashe, yau kwana 25 kenan ban sake jin muryarsa ba.
“Ni kadai ce yanzu a gida tare da yara, ina cikin tashin hankali matuka, da ta kai ko barci ba na iya yi, duk da cewa dai, na kan yi kokarin yin karfin hali, don kada yaran su firgita, amma ko shakka babu, muna cikin damuwa da tashin hankali kwarai da gaske.” Ta kara da cewa, daga baya aka sanar da ‘yan’uwa cewa; ana tuhumar mijin nata a kan kudi kusan naira miliyan biyu.
Ta ce, “An ce an toshe asusun ajiyarsa, wannan dalili ne ya sa ya tafi Abuja, domin a bude masa, daga baya kuma sai aka ce mana yana da alaka da da tuhuma a kan naira miliyan biyu.
Dan malamin, Sunusi Khalifa Sani Abdulkadir, wanda ya raka mahaifin nasa, ya bayyana abin da ya faru a tafiyar tasu zuwa Abuja.
Ya bayyana cewa, “Bayan an rufe asusun nasa, sai ya nemi dalilin da ya sa aka rufe, aka ce hukumar EFCC ce, sannan kuma za a iya bude asusun ne kadai, da zarar ya je ofishin nasu.
“Bayan sun yi wa shehin tambayoyi, sai suka ce akwai kudi kimanin naira miliyan biyu da aka aike masa, don haka suna kan yin bincike a kai, suka kara da cewa, wani ya hada shi da wani mutum da yake neman addu’o’in da suka shafi rayuwarsa, kuma ya aiwatar da addu’o’in kamar yadda ya nema.”
Ya kara da cewa, daga baya hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta bayyana lamarin a matsayin wanda ya shafi harkar sojoji.
Ya kara da cewa, “Binciken yana da alaka da sojoji, tuni kuma sun sanar da su, su ma sun ce mahaifin nawa ya amince a mayar da kudin, amma sai sojojin suka ce za su zo su yi masa tambayoyi, tun daga ranar; yanzu kwana 25 kenan ba mu sake ganinsa ba.















Discussion about this post