ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da ‘Yan Nijeriya Ke Bukata A 2026

by Leadership Hausa and Sulaiman
5 months ago
Nijeriya

A yayin da ‘yan Nijeriya suka shiga sabuwar shekarar 2026, sun bayyana godiyarsu, bisa raya su da Allah yayi, har suka ga shiga cikin sabuwar shekarar.

Shekarar ta 2025 ta kasance, cike take da manyan kalubale, musamman na kalubalen rashin tsaro, da ta addabi kasar.

2025, ta kuma kasance an fuskanci garkame makarantu da yawan samun yajin aikin manyan makarantu, musammman na gwamnati, wanda hakan ya haifar da jani in ja ka, a bangaren gwamnati da kuma kungiyoyin kwadado.

ADVERTISEMENT

Shekarar ta kuma zamo wacce a rinka sace dalibai, daga makarantunsu na kwana da kai hare-hare a cikin alumma da kuma kai wasu hare-haren, a guraren ibada.

Abin farko da ‘yan kasar suke fata a 2026 daga gun masu rike da madafun iko na siyasa a kasar shi ne, sauke nauyin da aka dora masu, na yin shugabanci, na gari.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Kazalika, yayin da zabukan 2027 ke kara karatowa, akasarin masu rike da madafun ikon, burinsu shi ne, su sake dare Karagarsu, inda tuni, tun kafin a kada Gangar siyasar, suka fara kai gauro da mari, domin ganin sun ci gaba da shugabantar alumomin su. Idan har suka ci gaba da yin wannan hakilon na son ci gaba da rike madafun iko na su, ba makawa, shugabancin, zai samu matsala,  wanda hakan zai kuma sanya, talakwan kasar, su ci gaba da ji a jikinsu.

Wani abin dubi a nan shi ne, yankin Arewacin kasar nan, ne ya fi fuskantar matsalar ta rashin tsaro, a fadin daukacin kasar.

Akasarin ‘yan Nijeriya dai, na fatan jami’an tsaro, su ci gaba da kamin da suke yi, na yakar ‘yan ta’adda da kuma kawo karshen aikata daukacin manyan laifuka.

Kasar dai, na ci gaba da zama a cikin fargabar hare-haren ‘yan bindiga daji da  na ‘yan ta’adda da masu yin garkuwa da mutane da kuma ci gaba da samun rikice-rikice, a cikin alumma, wanda hakan, ke ci gaba da tarwatsa tattalin arzikin kasar.

Hakazalika, abinda ‘yan kasar ke fata a 2026, shi ne, hada karfi da karfe, a tsakanin jami’an saro domin kawo karshen matsalar, musamman kuma a tabbatar da an yi gaskiya, wajen magance  kalubalen.

Dole ne a samar wa da jami’an tsaron kasar da kayan aiki, musamman domin su samu sukunin gudanar da aikinsu, na wanzar da tsaron rayuka da kuma dukiyoyin ‘yan kasar, inda yin hakan, ba zai sanya su rinka karbar na Goro, a gun masu yiwa tsaron kasar, zagon kasa ba.

Bugu da kari, ya kuma kamata Gwamnatin Tarayya ta nemi daukin kasashen waje, domin ta lalubo da mafita, kan kalubalen rashin tsaron kasar wanda kasar ta shafe shekaru 16, ta na fuskanta.

Koda yake dai, Gwamnatin shugaba Bola The Tinubu, ta fara daukar irin wannan matakin, duba da yadda ta nemi daukin kasar Amurka, inda Jiragen yakinta, suka kai munanan hare-hare kan sansanonin ‘yan bindiga da ke a jihar Sokoto.

Ya kamata kuma gwamnatin, ta kara fadada hadakar ta da Amurak, musamman wajen samun kayan yaki na zamani, domin ci gaba da yakar ‘yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda, musamman irinsu Al Kaeda da ISIS, da suka kusto cikin kasar, suke aikata ta’addancin su.

Hakazalika, ya wajaba kasar, ta nemi taimakaon kasasshn da take abotaka da su, domin ta murkushe ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga a 2026.

Dole ne kuma, Gwamnatin Bola Tinubu ta ajiye batun siyasa a gafe guda, domin ta yaki ‘yan ta’addar.

Yau a Nijeriya, ‘yan gudun hijira sun kai kimanin miliyan takwas, inda kuma wasu dubban mutane, ‘yan bindiga, ke ci gaba da rike su haka manoma da dama, basa iya zuwa gonakansu, domin noma su, saboda suna jin tsoron, kar a kashe su.

Zuba jari na kai tsaye daga ketare, zai taimaka wajen rage kangin talauci , musamman a  tsakanin talakwan kasar.

‘Yan Nijeriya ba wai kawai batun siyasa suke son ji, a fatar baki ba, amma suna sun su gani a kas.

Samar da fasahar zamani ta yin zabe musamman IREB, hakan ya sanya, ‘yan Nijeriya na da yakinin za a gudanar da sahihin zabe a 2027, musamman ganin yadda a zaben shugaban kasa na 2023, aka yiwa ‘yan Nijeriya, sakiyar da ba ruwa, ta hanyar lalata fatan da suke da shi, na samun shugabanci na gari.

Kan batun sauye-sauyen da aka samar na haraji ‘yan Nijeriya da dama, na fatan a gudanar da adalaci wajen aiwatar da sauye-sauyen.

‘Yan Nijeriya da dama dai, a 2026, na  fatan ganin cewa, kowanne dan kasar, ya amfana, ba wai kawai wasu ‘yan tsiraru kadai ne, za su amafana da ba.

Nijeriya
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe
Nijeriya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Nijeriya

Atiku Ya Fara Neman Mulki Tun Ina NYSC – Datti Baba-Ahmed

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.