A yayin da ‘yan Nijeriya suka shiga sabuwar shekarar 2026, sun bayyana godiyarsu, bisa raya su da Allah yayi, har suka ga shiga cikin sabuwar shekarar.
Shekarar ta 2025 ta kasance, cike take da manyan kalubale, musamman na kalubalen rashin tsaro, da ta addabi kasar.
2025, ta kuma kasance an fuskanci garkame makarantu da yawan samun yajin aikin manyan makarantu, musammman na gwamnati, wanda hakan ya haifar da jani in ja ka, a bangaren gwamnati da kuma kungiyoyin kwadado.
Shekarar ta kuma zamo wacce a rinka sace dalibai, daga makarantunsu na kwana da kai hare-hare a cikin alumma da kuma kai wasu hare-haren, a guraren ibada.
Abin farko da ‘yan kasar suke fata a 2026 daga gun masu rike da madafun iko na siyasa a kasar shi ne, sauke nauyin da aka dora masu, na yin shugabanci, na gari.
Kazalika, yayin da zabukan 2027 ke kara karatowa, akasarin masu rike da madafun ikon, burinsu shi ne, su sake dare Karagarsu, inda tuni, tun kafin a kada Gangar siyasar, suka fara kai gauro da mari, domin ganin sun ci gaba da shugabantar alumomin su. Idan har suka ci gaba da yin wannan hakilon na son ci gaba da rike madafun iko na su, ba makawa, shugabancin, zai samu matsala, wanda hakan zai kuma sanya, talakwan kasar, su ci gaba da ji a jikinsu.
Wani abin dubi a nan shi ne, yankin Arewacin kasar nan, ne ya fi fuskantar matsalar ta rashin tsaro, a fadin daukacin kasar.
Akasarin ‘yan Nijeriya dai, na fatan jami’an tsaro, su ci gaba da kamin da suke yi, na yakar ‘yan ta’adda da kuma kawo karshen aikata daukacin manyan laifuka.
Kasar dai, na ci gaba da zama a cikin fargabar hare-haren ‘yan bindiga daji da na ‘yan ta’adda da masu yin garkuwa da mutane da kuma ci gaba da samun rikice-rikice, a cikin alumma, wanda hakan, ke ci gaba da tarwatsa tattalin arzikin kasar.
Hakazalika, abinda ‘yan kasar ke fata a 2026, shi ne, hada karfi da karfe, a tsakanin jami’an saro domin kawo karshen matsalar, musamman kuma a tabbatar da an yi gaskiya, wajen magance kalubalen.
Dole ne a samar wa da jami’an tsaron kasar da kayan aiki, musamman domin su samu sukunin gudanar da aikinsu, na wanzar da tsaron rayuka da kuma dukiyoyin ‘yan kasar, inda yin hakan, ba zai sanya su rinka karbar na Goro, a gun masu yiwa tsaron kasar, zagon kasa ba.
Bugu da kari, ya kuma kamata Gwamnatin Tarayya ta nemi daukin kasashen waje, domin ta lalubo da mafita, kan kalubalen rashin tsaron kasar wanda kasar ta shafe shekaru 16, ta na fuskanta.
Koda yake dai, Gwamnatin shugaba Bola The Tinubu, ta fara daukar irin wannan matakin, duba da yadda ta nemi daukin kasar Amurka, inda Jiragen yakinta, suka kai munanan hare-hare kan sansanonin ‘yan bindiga da ke a jihar Sokoto.
Ya kamata kuma gwamnatin, ta kara fadada hadakar ta da Amurak, musamman wajen samun kayan yaki na zamani, domin ci gaba da yakar ‘yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda, musamman irinsu Al Kaeda da ISIS, da suka kusto cikin kasar, suke aikata ta’addancin su.
Hakazalika, ya wajaba kasar, ta nemi taimakaon kasasshn da take abotaka da su, domin ta murkushe ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga a 2026.
Dole ne kuma, Gwamnatin Bola Tinubu ta ajiye batun siyasa a gafe guda, domin ta yaki ‘yan ta’addar.
Yau a Nijeriya, ‘yan gudun hijira sun kai kimanin miliyan takwas, inda kuma wasu dubban mutane, ‘yan bindiga, ke ci gaba da rike su haka manoma da dama, basa iya zuwa gonakansu, domin noma su, saboda suna jin tsoron, kar a kashe su.
Zuba jari na kai tsaye daga ketare, zai taimaka wajen rage kangin talauci , musamman a tsakanin talakwan kasar.
‘Yan Nijeriya ba wai kawai batun siyasa suke son ji, a fatar baki ba, amma suna sun su gani a kas.
Samar da fasahar zamani ta yin zabe musamman IREB, hakan ya sanya, ‘yan Nijeriya na da yakinin za a gudanar da sahihin zabe a 2027, musamman ganin yadda a zaben shugaban kasa na 2023, aka yiwa ‘yan Nijeriya, sakiyar da ba ruwa, ta hanyar lalata fatan da suke da shi, na samun shugabanci na gari.
Kan batun sauye-sauyen da aka samar na haraji ‘yan Nijeriya da dama, na fatan a gudanar da adalaci wajen aiwatar da sauye-sauyen.
‘Yan Nijeriya da dama dai, a 2026, na fatan ganin cewa, kowanne dan kasar, ya amfana, ba wai kawai wasu ‘yan tsiraru kadai ne, za su amafana da ba.















Discussion about this post