ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Kashe Dan Ta’adda, Kachalla Kabiru A Jihar Kogi

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
5 months ago
Kachalla

Jami’an Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaro, Rundunar Sojin Kasa ta Nijeriya (Nigerian Army), da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (Department of State Services – DSS) sun kashe jagoran ‘yan bindiga, Kachalla Kabiru, tare da wasu manyan mataimakansa a wani samame na hadin gwiwa da aka kai a Jihar Kogi.

Majiyoyin tsaro masu inganci sun bayyana cewa an gudanar da wannan samame ne a ranar 13 ga Fabrairu, 2026, bayan makonni na tattara bayanan sirri da sa ido da suka tabbatar da kasancewar Kabiru a wani Boyayyen wuri da aka gano. Har ila yau, an yi amfani da hare-haren sama na musamman da Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya (Nigerian Air Force) ta kai domin kai farmakin.

  • Samar Da Motoci Masu Sulke: Ministan Tsaro Ya Yaba Da Jajircewar Gwamnan Zamfara A Fannin Tsaro
  • Ramadan: Hisbah Ta Kama Mutane 9 Bisa Zargin Cin Abinci A Bainar Jama’a

A cewar majiyar, “An kashe Kachalla Kabiru da wasu manyan mataimakansa a wani kakkarfan samame da ya hada da hare-haren sama da na kasa. An kai harin ne bayan sahihan bayanan sirri sun tabbatar da kasancewarsa a wurin da aka sa a gaba.”

ADVERTISEMENT

Majiyar ta kara da cewa Kabiru na taka muhimmiyar rawa wajen daukar ‘yan bindiga aiki, tsarawa da jagorantar zirga-zirgarsu a jihohi da dama na yankin Arewa ta Tsakiya da makwabtanta.

Ta kuma ce, “Kabiru ya bar yankin Arewa maso Yamma ya koma Kogi fiye da shekaru 10 da suka wuce, inda ya kafa sansani a cikin dazuka da al’ummomin kan iyaka. Daga nan ne yake jagorantar ayyukan garkuwa da mutane da ta’addanci a jihohin Kogi, Kwara, Benue, Enugu, Edo, Ekiti da Ondo. Ya kasance babban ginshiki da ke hada kungiyoyin masu aikata laifi a tsakanin jihohi.”

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Majiyar ta kara da cewa kashe Kabiru babban koma baya ne ga tsararrun ayyukan ‘yan bindiga a yankin Arewa ta Tsakiya, kuma ana sa ran hakan zai kawo tangarda ga hadin gwiwar ayyukan masu laifi.

Jami’an tsaron Nijeriya na ganin cewa Kabiru ya taka rawa sosai wajen samar da kayan aiki da daukar ma’aikata ga kungiyoyin ‘yan bindiga, tare da saukaka zirga-zirgar mayaka, makamai da wadanda aka sace ta hanyoyin dazuka daga Arewa maso Yamma zuwa yankunan Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Yamma.

Kachalla
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas
Kachalla
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC
  • Sulaiman
    Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
  • Sulaiman
    Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Sharuɗan Da Chelle Ya Gindaya Wa NFF Domin Cigaba Da Jagorantar Super Eagles 

Sharuɗan Da Chelle Ya Gindaya Wa NFF Domin Cigaba Da Jagorantar Super Eagles 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.