ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharuɗan Da Chelle Ya Gindaya Wa NFF Domin Cigaba Da Jagorantar Super Eagles 

by Rabilu Sanusi Bena
4 months ago
Chelle

A wani rahoto da Leadership Hausa ta tattato daga sauran jaridun cikin Gida, kocin babbar tawagar kwallon kafa ta Nijeriya (Super Eagles) Eric Chelle ya gindaya wasu sharudda ga hukumar kwallon kafa ta Nijeriya NFF matukar anason ya cigaba da kasancewa a matsayinsa na kocin Super Eagles, daga cikin sharudda 19 da tsohon kocin na tawagar kwallon kafa ta kasar Mali ya gindaya akwai karin albashi.

A yan kwanakinnan and danganta Chelle da komawa kungiyar kwallon kafa ta Olympic Marseille ta kasar Faransa, amma hakarsa bata cimma ruwa ba bayan kungiyar dake buga gasar Ligue 1 ta nada sabon koci, Eric Chelle ya sanya hannu kan kwantiragin shekaru biyu da NFF a watan Janairun shekarar 2025 tare da karin shekara daya idan yayi aikin mai kyau.

  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Dan Ta’adda, Kachalla Kabiru A Jihar Kogi
  • Rikicin Kabilanci A Jihar Ribas Ya Tayar Da Hankalin Al’umma

A cewar yar jaridar wasanni, Shina Oludare, kocin wanda yakeda shaidar dan kasa ta kasashe biyu ( Faransa da Mali) ya gabatar da sharudan da aka gabatar ga NFF a ranar 22 ga watan Janairun shekarar 2026, bayan abin da ya bayyana a matsayin tunani mai zurfi, inda ya bukaci a duba takardar da kyau a mayar masa da martani.

ADVERTISEMENT

Ga cikakken jerin sharudda 19 da Eric Chelle ya gabatar ga hukumar kwallon kafa ta Nijeriya (NFF)

1. Motar alfarma ta (SUV) tare da direba da jami’in tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

2. Gida a cikin unguwa mai tsaro tare da wutar lantarki ta awanni 24 ba tare da katsewa ba.

3. A tanadar mashi da ofishi mai dauke da kayan aiki na zamani.

4. Samar da ingantaccen intanet.

5. Tikitin jirgin sama ga matarshi da yaransa biyu.

6. Samar da na’urar GPS.

7. Samar da kayan aiki masu kyau bisa ga bukatar kocin.

8. Dangane da wasannin sada zumunta, kocin yana da yancin zabar wasannin sada zumunci da tawagar zata buga.

9. Kocin zai shirya yadda atisayen tawagar zai kasance.

10. Kocin zai gudanar da shirye-shirye domin ci gaban matasan yan wasa.

11. Samar wa kocin damar yin tafiya, kallo, da sa ido ga yan wasan Nijeriya dake buga wasa a Turai.

12. Samar wa kocin damar yin tafiya don kallon gasar kwallon kafa ta gida don gano yan wasa wadanda za a saka a cikin tawagar kasar a matakai daban-daban.

13. A daina tsoma masa baki wajen zabar yan wasan tawagar Super Eagles.

14. Hukumar NFF dole ne ta bayar da kwangilar aiki ga mataimakansa.

15. Ana bukatar biyan albashi a ranar 30 ga kowane wata ko kafin ranar 30 ga wata.

16. Karin albashi da alawus kamar yadda tsarin tawagar ya tanada.

17. Bukatar a saka babban hadiminsa a cikin tsarin alawus.

18. Albashin dala $130,000.00 (dala dubu ɗari da talatin) kowane wata, inda zai kunshi sauran mataimakansa.

19. Ganawa ta wata-wata da dukkan masu horar da sauran tawagogin kwallon kafa a kasar.

Chelle
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

MASU ALAKA

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
Wasanni

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 3

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.