ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Karuwar Hada-hadar Jiragen Ruwa A Zangon Farko Na 2026 —Shugaban NPA

by Abubakar Abba
1 month ago
NPA

A zango na farko na shekarar 2026, fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar nan, ya fara da kafar dama, musamman duba da yadda aka samu zirga-zirgar Jiragen Ruwa da suka karu zuwa  jimlar, metric tan miliyan 32.38, tare da kuma samun karuwar kaso,  67 na hada-hadar shigo da ababen hawa.

A cikin rahoton nazari, na kokarin da aka samu a hukumar a zango na daya na 2026 wanda NPA ta fitar ya nuna cewa, hada-hadar shiga da fitar da kaya daga Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, cikin kayan ban da Danyen Mai, sun karu zuwa jimlar kaso 11.6 daga kaso metric tan miliyan 29.02.

Kazalika, rahoton ya nuna cewa, an samu karuwa a tsarin yiwa Jiragen Ruwa rijista wato GRT, wanda ya daga kai kaso 19.5 zuwa kaso niliyan  46.75.

ADVERTISEMENT

A cewar NPA sauye-sauyen da a aka ci gaba da samar wa da kuma karin bukatar da ake da ita a bangren shige da ficen Jiragen Ruwa na kasashen waje zuwa cikin kasar da kuma aikin kananan Tashoshin Jiragen Ruwa na Lekki, sun kara taimaka wa, wajen samun wadannan nasarorin.

Bugu da kari, ci gaba da namjin kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na sayen kayan aiki na zamani a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, hakan ya kara daga darajar kasar nan a hada-hadar kasuwanci na Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

A kwanan  baya, an ruwaito Shugaban Hukumar NPA Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, ya zama wajibi, Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar su ci gaba da gudanar da gasa, a harkar sufurin Jiragen Ruwa a nahiyar Afirka.

Dantsoho ya bayyana haka ne a wani taro kungiyar masu masana’antu, da aka gudanar a jihar Legas.

“Irin tsarin da muka samar a fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar nan, hakan na ci gaba da taimaka wa matuka, wajen kara habaka fannin tattalin arzikin kasar,” Inji Dantsoho.

Kazalika, rahoton ya nuna cewa, an samu karin da ya kai daga kaso 23.7 zuwa kaso 14.13 na   metric tan miliyan na hinTa-hadar kasuwanci na yanki.

Kazalika, hada-hadar shige da ficen Jiragen da suna yo jigilar kwantaina, ya karu daga kaso zuwa 67.6 zuwa kaso 102,803.

Hakazalika, an kuma samu nasara wajen shigo da ababen hawa, inda suka karu daga kaso 67 zuwa kaso 58,870, musamman idan aka kwatanta da wanda aka samu a bara, da suka kai kaso 35,262 .

Sauye-sauyen da a kirkiro da su a karkashin gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, musamman na zamantakewar da Tashoshin Jiragen Ruwan kasar hakan ya kara taimaka wa fannin.

Manyan sauye-sauyen su ne na aikin sabunta ginin Tashoshin Jiragen Ruwa na Legas da na Tin Can Island, musamman bayan amincewa tare da kuma sanya hannun yarjejeniyar ta dala biliyan daya.

Ministan Bunkasa Fannin Tattalin Arziki na Teku Adegboyega Oyetola ya bayyana cewa,  ana kan shirye-shiyen sayo wasu kayan aiki domin a daga darajar Tashoshin Jiragen Ruwa na Warri da ta, Onne da kuma ta Kalaba.

Samar da tsare-tsaren kara daga daraja da kuma kimar kayan aiki a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, wadanda suka kasance na zamani ta hanyar amfani da NSW da kuma PCS, sun kara taimaka wa wajen magance jinkiri da kuma kara tabbatar da ana bin ka’ida.

 Masu ruwa da tsaki a fannin masana’antu, suma ba a bar su a baya ba, wajen bayyana yakinin su na cewa, nasarorin da aka samu, sun kara taimaka wa, wajen samar da saukin hada-hadar kasuwanci a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.

Bugu da kari, gwamnatin tarayya ta kara fadada fannin zuba jari a Tashoshin kan tudu wanda hakan ya sanya fannin, ke ci gaba da habaka tare da kuma rage yawan yadda a baya, ake samun cunkoso Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

Hakazalika, karfafa tsaro da aka yi a hanyoyin Ruwan kasar hakan ya kara tabbatar da kwarin guwai, ga fannin.

Babbar hujja kan wannan batun shi ne, ganin yadda yau Nijeriya ta shafe shekaru hudu, ba samu masu fashin Teku ba.

Sai dai, duk da irin wannan dimbin nasarorin da aka samu a fannin, shugaban hukumar ta NPA, har yanzu, akwai sauran aiki, da ya kai kaso 25 na cunkoson Jiragen Ruwa da ake ci gaba da fuskanta a Afirka ta Yamma.

Ya kara da cewa, duk da wadannan nasarorin, da suka kai na sama da kaso 60 na tattalin arzikin yankin, ya zama wajibi Nijeriya ta ci gaba da samar da sauye-sauyen da kara habaka fannin sufurin Jiragen Ruwan kasar.

NPA
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan

Kotu Za Ta Saurari Ƙarar Da Ke Ƙalubalantar Cancantar Tsayawar Jonathan Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.