ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Karuwar Hada-hadar Jiragen Ruwa A Zangon Farko Na 2026 —Shugaban NPA

by Abubakar Abba
3 weeks ago
NPA

A zango na farko na shekarar 2026, fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar nan, ya fara da kafar dama, musamman duba da yadda aka samu zirga-zirgar Jiragen Ruwa da suka karu zuwa  jimlar, metric tan miliyan 32.38, tare da kuma samun karuwar kaso,  67 na hada-hadar shigo da ababen hawa.

A cikin rahoton nazari, na kokarin da aka samu a hukumar a zango na daya na 2026 wanda NPA ta fitar ya nuna cewa, hada-hadar shiga da fitar da kaya daga Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, cikin kayan ban da Danyen Mai, sun karu zuwa jimlar kaso 11.6 daga kaso metric tan miliyan 29.02.

Kazalika, rahoton ya nuna cewa, an samu karuwa a tsarin yiwa Jiragen Ruwa rijista wato GRT, wanda ya daga kai kaso 19.5 zuwa kaso niliyan  46.75.

ADVERTISEMENT

A cewar NPA sauye-sauyen da a aka ci gaba da samar wa da kuma karin bukatar da ake da ita a bangren shige da ficen Jiragen Ruwa na kasashen waje zuwa cikin kasar da kuma aikin kananan Tashoshin Jiragen Ruwa na Lekki, sun kara taimaka wa, wajen samun wadannan nasarorin.

Bugu da kari, ci gaba da namjin kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na sayen kayan aiki na zamani a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, hakan ya kara daga darajar kasar nan a hada-hadar kasuwanci na Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

A kwanan  baya, an ruwaito Shugaban Hukumar NPA Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, ya zama wajibi, Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar su ci gaba da gudanar da gasa, a harkar sufurin Jiragen Ruwa a nahiyar Afirka.

Dantsoho ya bayyana haka ne a wani taro kungiyar masu masana’antu, da aka gudanar a jihar Legas.

“Irin tsarin da muka samar a fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar nan, hakan na ci gaba da taimaka wa matuka, wajen kara habaka fannin tattalin arzikin kasar,” Inji Dantsoho.

Kazalika, rahoton ya nuna cewa, an samu karin da ya kai daga kaso 23.7 zuwa kaso 14.13 na   metric tan miliyan na hinTa-hadar kasuwanci na yanki.

Kazalika, hada-hadar shige da ficen Jiragen da suna yo jigilar kwantaina, ya karu daga kaso zuwa 67.6 zuwa kaso 102,803.

Hakazalika, an kuma samu nasara wajen shigo da ababen hawa, inda suka karu daga kaso 67 zuwa kaso 58,870, musamman idan aka kwatanta da wanda aka samu a bara, da suka kai kaso 35,262 .

Sauye-sauyen da a kirkiro da su a karkashin gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, musamman na zamantakewar da Tashoshin Jiragen Ruwan kasar hakan ya kara taimaka wa fannin.

Manyan sauye-sauyen su ne na aikin sabunta ginin Tashoshin Jiragen Ruwa na Legas da na Tin Can Island, musamman bayan amincewa tare da kuma sanya hannun yarjejeniyar ta dala biliyan daya.

Ministan Bunkasa Fannin Tattalin Arziki na Teku Adegboyega Oyetola ya bayyana cewa,  ana kan shirye-shiyen sayo wasu kayan aiki domin a daga darajar Tashoshin Jiragen Ruwa na Warri da ta, Onne da kuma ta Kalaba.

Samar da tsare-tsaren kara daga daraja da kuma kimar kayan aiki a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, wadanda suka kasance na zamani ta hanyar amfani da NSW da kuma PCS, sun kara taimaka wa wajen magance jinkiri da kuma kara tabbatar da ana bin ka’ida.

 Masu ruwa da tsaki a fannin masana’antu, suma ba a bar su a baya ba, wajen bayyana yakinin su na cewa, nasarorin da aka samu, sun kara taimaka wa, wajen samar da saukin hada-hadar kasuwanci a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.

Bugu da kari, gwamnatin tarayya ta kara fadada fannin zuba jari a Tashoshin kan tudu wanda hakan ya sanya fannin, ke ci gaba da habaka tare da kuma rage yawan yadda a baya, ake samun cunkoso Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

Hakazalika, karfafa tsaro da aka yi a hanyoyin Ruwan kasar hakan ya kara tabbatar da kwarin guwai, ga fannin.

Babbar hujja kan wannan batun shi ne, ganin yadda yau Nijeriya ta shafe shekaru hudu, ba samu masu fashin Teku ba.

Sai dai, duk da irin wannan dimbin nasarorin da aka samu a fannin, shugaban hukumar ta NPA, har yanzu, akwai sauran aiki, da ya kai kaso 25 na cunkoson Jiragen Ruwa da ake ci gaba da fuskanta a Afirka ta Yamma.

Ya kara da cewa, duk da wadannan nasarorin, da suka kai na sama da kaso 60 na tattalin arzikin yankin, ya zama wajibi Nijeriya ta ci gaba da samar da sauye-sauyen da kara habaka fannin sufurin Jiragen Ruwan kasar.

NPA
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tattalin Arziki

Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas

May 24, 2026
Next Post
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan

Kotu Za Ta Saurari Ƙarar Da Ke Ƙalubalantar Cancantar Tsayawar Jonathan Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.