ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Ta Kafa Kwamitin Sasanta Rikicin Manoma Da Makiyaya

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Yahaya, ya ce gwamnatinsa ta samar da cikakken tsari na musamman, wanda aka rubuta a cikin ‘White Paper’, domin daƙile rikice-rikicen manoma da makiyaya, ’yian bindiga da sauran ƙalubalen tsaro masu alaƙa da su.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin ƙaddamar da wani babban kwamitin aiwatar da White Paper kan wuraren kiwo, gandun daji da wuraren ajiyar namun daji, da kuma hanyoyin shanu a jihar.

Kwamitin ya ƙunshi ƙwararru a fannin tsaro, lauyoyi da masana fasahar taswira, kuma an ɗora musu alhakin fassara manufofin gwamnati zuwa ayyuka na zahiri da za a iya aiwatarwa da kuma tilastawa bin doka.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Ta’aziyyar Mutane 5 Da Suka Rasu A Hatsarin Mota 
  • Yadda Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan ‘Yan Jarida 7 A Gombe 

Gwamnan ya bayyana cewa kafa kwamitin ya biyo bayan aikin wani kwamitin tantancewa da gwamnatinsa ta kafa tun da farko, wanda ya duba matsalolin da ke tattare da wuraren kiwo, gandun daji da wuraren ajiyar namun daji, da kuma hanyoyin shanu, da nufin samar da hanyoyin warware matsalolin da za su kasance masu amfani kuma masu ɗorewa.

Sakamakon bincike da shawarwarin kwamitin tantancewar sun samu amincewar Majalisar Zartarwa ta Jihar, sannan aka fayyace su a cikin White Paper.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

A cewar gwamnan, wannan shiri na da nufin kawar da tsofaffin hanyoyin kiwo marasa tsari, ƙarfafa tsaro da tsarin doka, da kuma hana rikice-rikicen manoma da makiyaya, tare da tabbatar da wadatar abinci da zaman lafiya da jituwa a faɗin jihar.

“Xaya daga cikin manyan matsalolin da ke ci gaba da addabar Arewacin Nijeriya, har ma da ƙasar baki ɗaya, shi ne rikice-rikicen manoma da makiyaya da ke faruwa akai-akai, wanda yawanci ke samo asali daga taƙaddama kan ƙasa da albarkatu, musamman a lokacin girbi,” in ji gwamnan.

Ya ƙara da cewa, “Mamaye wuraren kiwo, gandun daji da hanyoyin shanu ya ƙara tsananta lamarin, kuma gazawar gwamnatoci da suka gabata wajen magance wannan matsala da irin ƙarfin siyasar da ya dace ba abin takaici kaɗai ba ne, abin Allah-wadai ne.”

Yahaya ya bayyana cewa duk da yawaitar al’ummar Nijeriya cikin sauri, akwai faɗaɗɗun ƙasashe masu yawa da har yanzu ba a noma su ba kuma ba a amfani da su yadda ya kamata.

Ya jaddada cewa ana iya amfani da irin waɗannan albarkatu yadda ya dace domin zamanantar da kiwon dabbobi, taƙaita kiwo a wuri guda, da kuma kawo ƙarshen dogon yawo da shanu ke yi wanda ke haddasa matsalolin tsaro, ’yan bindiga da garkuwa da mutane.

Ya kuma bayyana cewa ƙudurin gwamnatinsa na dawo da wuraren kiwo, gandun daji da hanyoyin shanu da aka rasa ko aka mamaye na daga cikin muhimman hanyoyin rage rikici da kare rayuwar manoma da makiyaya.

Da yake nuna cewa sama da kashi 80 cikin 100 na al’ummar jihar na dogaro da noma da kiwon dabbobi, gwamnan ya ce ya zama dole gwamnati ta nuna ƙarfin siyasa domin kare rayuka, dukiyoyi da kuma bunƙasar tattalin arziki.

Yahaya, wanda shi ne kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, ya bayyana ƙwarin gwiwa cewa rungumar hanyoyin kiwo na zamani da kuma kawar da tsofaffin hanyoyin kiwon dabbobi za su samar da sabon tsari ba ga Jihar Gombe kaɗai ba, har ma ga Arewacin Nijeriya da ƙasar baki ɗaya.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf: "Allah Ne Ya Sanya Ni Gwamna, Muradun Kano Ne Gaba, Ba Biyayya Ga Wani Ba"

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.