ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Ta Kafa Kwamitin Sasanta Rikicin Manoma Da Makiyaya

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Yahaya, ya ce gwamnatinsa ta samar da cikakken tsari na musamman, wanda aka rubuta a cikin ‘White Paper’, domin daƙile rikice-rikicen manoma da makiyaya, ’yian bindiga da sauran ƙalubalen tsaro masu alaƙa da su.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin ƙaddamar da wani babban kwamitin aiwatar da White Paper kan wuraren kiwo, gandun daji da wuraren ajiyar namun daji, da kuma hanyoyin shanu a jihar.

Kwamitin ya ƙunshi ƙwararru a fannin tsaro, lauyoyi da masana fasahar taswira, kuma an ɗora musu alhakin fassara manufofin gwamnati zuwa ayyuka na zahiri da za a iya aiwatarwa da kuma tilastawa bin doka.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Ta’aziyyar Mutane 5 Da Suka Rasu A Hatsarin Mota 
  • Yadda Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan ‘Yan Jarida 7 A Gombe 

Gwamnan ya bayyana cewa kafa kwamitin ya biyo bayan aikin wani kwamitin tantancewa da gwamnatinsa ta kafa tun da farko, wanda ya duba matsalolin da ke tattare da wuraren kiwo, gandun daji da wuraren ajiyar namun daji, da kuma hanyoyin shanu, da nufin samar da hanyoyin warware matsalolin da za su kasance masu amfani kuma masu ɗorewa.

Sakamakon bincike da shawarwarin kwamitin tantancewar sun samu amincewar Majalisar Zartarwa ta Jihar, sannan aka fayyace su a cikin White Paper.

LABARAI MASU NASABA

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

A cewar gwamnan, wannan shiri na da nufin kawar da tsofaffin hanyoyin kiwo marasa tsari, ƙarfafa tsaro da tsarin doka, da kuma hana rikice-rikicen manoma da makiyaya, tare da tabbatar da wadatar abinci da zaman lafiya da jituwa a faɗin jihar.

“Xaya daga cikin manyan matsalolin da ke ci gaba da addabar Arewacin Nijeriya, har ma da ƙasar baki ɗaya, shi ne rikice-rikicen manoma da makiyaya da ke faruwa akai-akai, wanda yawanci ke samo asali daga taƙaddama kan ƙasa da albarkatu, musamman a lokacin girbi,” in ji gwamnan.

Ya ƙara da cewa, “Mamaye wuraren kiwo, gandun daji da hanyoyin shanu ya ƙara tsananta lamarin, kuma gazawar gwamnatoci da suka gabata wajen magance wannan matsala da irin ƙarfin siyasar da ya dace ba abin takaici kaɗai ba ne, abin Allah-wadai ne.”

Yahaya ya bayyana cewa duk da yawaitar al’ummar Nijeriya cikin sauri, akwai faɗaɗɗun ƙasashe masu yawa da har yanzu ba a noma su ba kuma ba a amfani da su yadda ya kamata.

Ya jaddada cewa ana iya amfani da irin waɗannan albarkatu yadda ya dace domin zamanantar da kiwon dabbobi, taƙaita kiwo a wuri guda, da kuma kawo ƙarshen dogon yawo da shanu ke yi wanda ke haddasa matsalolin tsaro, ’yan bindiga da garkuwa da mutane.

Ya kuma bayyana cewa ƙudurin gwamnatinsa na dawo da wuraren kiwo, gandun daji da hanyoyin shanu da aka rasa ko aka mamaye na daga cikin muhimman hanyoyin rage rikici da kare rayuwar manoma da makiyaya.

Da yake nuna cewa sama da kashi 80 cikin 100 na al’ummar jihar na dogaro da noma da kiwon dabbobi, gwamnan ya ce ya zama dole gwamnati ta nuna ƙarfin siyasa domin kare rayuka, dukiyoyi da kuma bunƙasar tattalin arziki.

Yahaya, wanda shi ne kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, ya bayyana ƙwarin gwiwa cewa rungumar hanyoyin kiwo na zamani da kuma kawar da tsofaffin hanyoyin kiwon dabbobi za su samar da sabon tsari ba ga Jihar Gombe kaɗai ba, har ma ga Arewacin Nijeriya da ƙasar baki ɗaya.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara
Labarai

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
Tsaro

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
Labarai

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Next Post
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf: "Allah Ne Ya Sanya Ni Gwamna, Muradun Kano Ne Gaba, Ba Biyayya Ga Wani Ba"

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin: Za a Gudanar Da Bukukuwa Fiye Da 100 Na “Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasar Sin” a Shekara Ta 2026

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin: Za a Gudanar Da Bukukuwa Fiye Da 100 Na “Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasar Sin” a Shekara Ta 2026

June 5, 2026
Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki A DPRK

Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki A DPRK

June 5, 2026
Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

June 5, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.