ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Ta Kafa Kwamitin Sasanta Rikicin Manoma Da Makiyaya

by Rabi'u Ali Indabawa
8 months ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Yahaya, ya ce gwamnatinsa ta samar da cikakken tsari na musamman, wanda aka rubuta a cikin ‘White Paper’, domin daƙile rikice-rikicen manoma da makiyaya, ’yian bindiga da sauran ƙalubalen tsaro masu alaƙa da su.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin ƙaddamar da wani babban kwamitin aiwatar da White Paper kan wuraren kiwo, gandun daji da wuraren ajiyar namun daji, da kuma hanyoyin shanu a jihar.

Kwamitin ya ƙunshi ƙwararru a fannin tsaro, lauyoyi da masana fasahar taswira, kuma an ɗora musu alhakin fassara manufofin gwamnati zuwa ayyuka na zahiri da za a iya aiwatarwa da kuma tilastawa bin doka.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Ta’aziyyar Mutane 5 Da Suka Rasu A Hatsarin Mota 
  • Yadda Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan ‘Yan Jarida 7 A Gombe 

Gwamnan ya bayyana cewa kafa kwamitin ya biyo bayan aikin wani kwamitin tantancewa da gwamnatinsa ta kafa tun da farko, wanda ya duba matsalolin da ke tattare da wuraren kiwo, gandun daji da wuraren ajiyar namun daji, da kuma hanyoyin shanu, da nufin samar da hanyoyin warware matsalolin da za su kasance masu amfani kuma masu ɗorewa.

Sakamakon bincike da shawarwarin kwamitin tantancewar sun samu amincewar Majalisar Zartarwa ta Jihar, sannan aka fayyace su a cikin White Paper.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

A cewar gwamnan, wannan shiri na da nufin kawar da tsofaffin hanyoyin kiwo marasa tsari, ƙarfafa tsaro da tsarin doka, da kuma hana rikice-rikicen manoma da makiyaya, tare da tabbatar da wadatar abinci da zaman lafiya da jituwa a faɗin jihar.

“Xaya daga cikin manyan matsalolin da ke ci gaba da addabar Arewacin Nijeriya, har ma da ƙasar baki ɗaya, shi ne rikice-rikicen manoma da makiyaya da ke faruwa akai-akai, wanda yawanci ke samo asali daga taƙaddama kan ƙasa da albarkatu, musamman a lokacin girbi,” in ji gwamnan.

Ya ƙara da cewa, “Mamaye wuraren kiwo, gandun daji da hanyoyin shanu ya ƙara tsananta lamarin, kuma gazawar gwamnatoci da suka gabata wajen magance wannan matsala da irin ƙarfin siyasar da ya dace ba abin takaici kaɗai ba ne, abin Allah-wadai ne.”

Yahaya ya bayyana cewa duk da yawaitar al’ummar Nijeriya cikin sauri, akwai faɗaɗɗun ƙasashe masu yawa da har yanzu ba a noma su ba kuma ba a amfani da su yadda ya kamata.

Ya jaddada cewa ana iya amfani da irin waɗannan albarkatu yadda ya dace domin zamanantar da kiwon dabbobi, taƙaita kiwo a wuri guda, da kuma kawo ƙarshen dogon yawo da shanu ke yi wanda ke haddasa matsalolin tsaro, ’yan bindiga da garkuwa da mutane.

Ya kuma bayyana cewa ƙudurin gwamnatinsa na dawo da wuraren kiwo, gandun daji da hanyoyin shanu da aka rasa ko aka mamaye na daga cikin muhimman hanyoyin rage rikici da kare rayuwar manoma da makiyaya.

Da yake nuna cewa sama da kashi 80 cikin 100 na al’ummar jihar na dogaro da noma da kiwon dabbobi, gwamnan ya ce ya zama dole gwamnati ta nuna ƙarfin siyasa domin kare rayuka, dukiyoyi da kuma bunƙasar tattalin arziki.

Yahaya, wanda shi ne kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, ya bayyana ƙwarin gwiwa cewa rungumar hanyoyin kiwo na zamani da kuma kawar da tsofaffin hanyoyin kiwon dabbobi za su samar da sabon tsari ba ga Jihar Gombe kaɗai ba, har ma ga Arewacin Nijeriya da ƙasar baki ɗaya.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf: "Allah Ne Ya Sanya Ni Gwamna, Muradun Kano Ne Gaba, Ba Biyayya Ga Wani Ba"

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.