ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Ta Kafa Kwamitin Sasanta Rikicin Manoma Da Makiyaya

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Yahaya, ya ce gwamnatinsa ta samar da cikakken tsari na musamman, wanda aka rubuta a cikin ‘White Paper’, domin daƙile rikice-rikicen manoma da makiyaya, ’yian bindiga da sauran ƙalubalen tsaro masu alaƙa da su.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin ƙaddamar da wani babban kwamitin aiwatar da White Paper kan wuraren kiwo, gandun daji da wuraren ajiyar namun daji, da kuma hanyoyin shanu a jihar.

Kwamitin ya ƙunshi ƙwararru a fannin tsaro, lauyoyi da masana fasahar taswira, kuma an ɗora musu alhakin fassara manufofin gwamnati zuwa ayyuka na zahiri da za a iya aiwatarwa da kuma tilastawa bin doka.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Ta’aziyyar Mutane 5 Da Suka Rasu A Hatsarin Mota 
  • Yadda Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan ‘Yan Jarida 7 A Gombe 

Gwamnan ya bayyana cewa kafa kwamitin ya biyo bayan aikin wani kwamitin tantancewa da gwamnatinsa ta kafa tun da farko, wanda ya duba matsalolin da ke tattare da wuraren kiwo, gandun daji da wuraren ajiyar namun daji, da kuma hanyoyin shanu, da nufin samar da hanyoyin warware matsalolin da za su kasance masu amfani kuma masu ɗorewa.

Sakamakon bincike da shawarwarin kwamitin tantancewar sun samu amincewar Majalisar Zartarwa ta Jihar, sannan aka fayyace su a cikin White Paper.

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

A cewar gwamnan, wannan shiri na da nufin kawar da tsofaffin hanyoyin kiwo marasa tsari, ƙarfafa tsaro da tsarin doka, da kuma hana rikice-rikicen manoma da makiyaya, tare da tabbatar da wadatar abinci da zaman lafiya da jituwa a faɗin jihar.

“Xaya daga cikin manyan matsalolin da ke ci gaba da addabar Arewacin Nijeriya, har ma da ƙasar baki ɗaya, shi ne rikice-rikicen manoma da makiyaya da ke faruwa akai-akai, wanda yawanci ke samo asali daga taƙaddama kan ƙasa da albarkatu, musamman a lokacin girbi,” in ji gwamnan.

Ya ƙara da cewa, “Mamaye wuraren kiwo, gandun daji da hanyoyin shanu ya ƙara tsananta lamarin, kuma gazawar gwamnatoci da suka gabata wajen magance wannan matsala da irin ƙarfin siyasar da ya dace ba abin takaici kaɗai ba ne, abin Allah-wadai ne.”

Yahaya ya bayyana cewa duk da yawaitar al’ummar Nijeriya cikin sauri, akwai faɗaɗɗun ƙasashe masu yawa da har yanzu ba a noma su ba kuma ba a amfani da su yadda ya kamata.

Ya jaddada cewa ana iya amfani da irin waɗannan albarkatu yadda ya dace domin zamanantar da kiwon dabbobi, taƙaita kiwo a wuri guda, da kuma kawo ƙarshen dogon yawo da shanu ke yi wanda ke haddasa matsalolin tsaro, ’yan bindiga da garkuwa da mutane.

Ya kuma bayyana cewa ƙudurin gwamnatinsa na dawo da wuraren kiwo, gandun daji da hanyoyin shanu da aka rasa ko aka mamaye na daga cikin muhimman hanyoyin rage rikici da kare rayuwar manoma da makiyaya.

Da yake nuna cewa sama da kashi 80 cikin 100 na al’ummar jihar na dogaro da noma da kiwon dabbobi, gwamnan ya ce ya zama dole gwamnati ta nuna ƙarfin siyasa domin kare rayuka, dukiyoyi da kuma bunƙasar tattalin arziki.

Yahaya, wanda shi ne kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, ya bayyana ƙwarin gwiwa cewa rungumar hanyoyin kiwo na zamani da kuma kawar da tsofaffin hanyoyin kiwon dabbobi za su samar da sabon tsari ba ga Jihar Gombe kaɗai ba, har ma ga Arewacin Nijeriya da ƙasar baki ɗaya.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf: "Allah Ne Ya Sanya Ni Gwamna, Muradun Kano Ne Gaba, Ba Biyayya Ga Wani Ba"

LABARAI MASU NASABA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.