ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Matasa Za Su Yi Wa Talauci Layar-zana -Farfesa Adedimeji

by Sani Anwar
6 months ago
Farfesa

Mataimakin Shugaban Makarantar Nazarin Tattalin Arziƙi ta Afirka da ke Abuja, Farfesa Mahfouz Adedimeji, ya buƙaci ƴan Nijeriya, musamman matasa da su ɗauki matakan da za su taimaka musu wajen kawar da talauci da kuma taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

A cewar mataimakin shugaban, ana kafa gwamnati ne, domin magance buƙatun al’umma, waɗanda a farko suka haɗa da abinci, sutura da kuma matsuguni, wanda dukkaninsu sashe ne tattalin arziƙi.

  • Jakadan Sin Ya Gana Da Shugaba Tinubu, Inda Ya Jaddada Alkawarin Sin Na Karfafa Alaka Da Nijeriya
  • Sin Ta Baiwa Kauyen Gwaji Na Rage Talauci Na Sin Da Habasha Na’urorin Aikin Noma

Ya ƙara da cewa, idan har aka magance muhimman buƙatu na tattalin arziƙi, babu shakka za a iya shawo kan ƙalubale da dama wanda miliyoyin mutane ke fuskanta, inda ya ƙara da cewa; wannan falsafar ta ɗauki nauyin shigar da ilimin tattalin arziƙi a matsayin ginshiƙin horas da ɗalibai, ba tare da la’akari da nau’o’insu ba. Shugaban ya bayyana wannan tsari a matsayin ilimin da ke keɓe a jami’a.

ADVERTISEMENT

Yayin da yake bayyana mummunan talauci a matsayin wanni nau’i na rashin ilimi da cikakkiyar lafiya, rashin isasshiyar rayuwa da rashin samun damar yin amfani da kayan amfani na yau da kullum, Farfesa Adedimeji ya ce; guje wa talauci ga mutane, musamman matasa na buƙatar haɓaka aiki ta hanyar ilimi, samar da samfurorin kasuwa da kuma samun basirar da ke haifar da samun kuɗin shiga ko yin aikin da za a biya mutum kuɗi.

Don, wanda ƙwararre ne a fannin ilmin kimiyya ta duniya, kuma jami’in hukumar kula da hada-hadar kuɗi ta Nijeriya, ya kuma jaddada cewa; rage kashe kuɗaɗe da kuma ƙara yawan kuɗaɗen shiga, dabaru ne guda biyu da aka gwada lokaci bayan lokaci na shawo kan matsalar tattalin arziƙi tare da ƙarfafa wa matasa gwiwa, wajen koyon dabi’ar sa kai, domin yana daga cikin samun ƙwarewa da kuma jawo hankalin masu zuwa a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Farfesa Adedimeji ya gabatar da cewa, gyare-gyaren da gwamnatin tarayya ta yi a ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, na nuna wasu kyawawan alamu; domin a hankali darajar naira ta ƙaru idan aka kwatanta da kuɗaɗen ƙasashen waje a baya.

Har ila yau, babbar hanyar samun ci gaba ga Nijeriya, a cewarsa; ta ta’allaƙa ne da fannoni daban-daban na tattalin arziƙi, bunƙasa ilimi da sana’o’i, inganta harkokin kiwon lafiya, cibiyoyin tsaro na zamantakewa, samar da ababen more rayuwa da kuma samar da kyakkyawan shugabanci da riƙon amana.

Sannan, ya kuma buƙaci ƴan Nijeriya da su rungumi dabi’ar yin aiki tuƙuru, kana kuma su kasance masu imani, amana, haƙuri da kuma fata na gari.

 

Farfesa
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Next Post
Makonni Biyu Bayan Sace Ɗaliban Makarantar Papiri A Neja, Har Yanzu Babu Tuntuɓa

Makonni Biyu Bayan Sace Ɗaliban Makarantar Papiri A Neja, Har Yanzu Babu Tuntuɓa

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.