ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Matasa Za Su Yi Wa Talauci Layar-zana -Farfesa Adedimeji

by Sani Anwar
7 months ago
Farfesa

Mataimakin Shugaban Makarantar Nazarin Tattalin Arziƙi ta Afirka da ke Abuja, Farfesa Mahfouz Adedimeji, ya buƙaci ƴan Nijeriya, musamman matasa da su ɗauki matakan da za su taimaka musu wajen kawar da talauci da kuma taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

A cewar mataimakin shugaban, ana kafa gwamnati ne, domin magance buƙatun al’umma, waɗanda a farko suka haɗa da abinci, sutura da kuma matsuguni, wanda dukkaninsu sashe ne tattalin arziƙi.

  • Jakadan Sin Ya Gana Da Shugaba Tinubu, Inda Ya Jaddada Alkawarin Sin Na Karfafa Alaka Da Nijeriya
  • Sin Ta Baiwa Kauyen Gwaji Na Rage Talauci Na Sin Da Habasha Na’urorin Aikin Noma

Ya ƙara da cewa, idan har aka magance muhimman buƙatu na tattalin arziƙi, babu shakka za a iya shawo kan ƙalubale da dama wanda miliyoyin mutane ke fuskanta, inda ya ƙara da cewa; wannan falsafar ta ɗauki nauyin shigar da ilimin tattalin arziƙi a matsayin ginshiƙin horas da ɗalibai, ba tare da la’akari da nau’o’insu ba. Shugaban ya bayyana wannan tsari a matsayin ilimin da ke keɓe a jami’a.

ADVERTISEMENT

Yayin da yake bayyana mummunan talauci a matsayin wanni nau’i na rashin ilimi da cikakkiyar lafiya, rashin isasshiyar rayuwa da rashin samun damar yin amfani da kayan amfani na yau da kullum, Farfesa Adedimeji ya ce; guje wa talauci ga mutane, musamman matasa na buƙatar haɓaka aiki ta hanyar ilimi, samar da samfurorin kasuwa da kuma samun basirar da ke haifar da samun kuɗin shiga ko yin aikin da za a biya mutum kuɗi.

Don, wanda ƙwararre ne a fannin ilmin kimiyya ta duniya, kuma jami’in hukumar kula da hada-hadar kuɗi ta Nijeriya, ya kuma jaddada cewa; rage kashe kuɗaɗe da kuma ƙara yawan kuɗaɗen shiga, dabaru ne guda biyu da aka gwada lokaci bayan lokaci na shawo kan matsalar tattalin arziƙi tare da ƙarfafa wa matasa gwiwa, wajen koyon dabi’ar sa kai, domin yana daga cikin samun ƙwarewa da kuma jawo hankalin masu zuwa a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Farfesa Adedimeji ya gabatar da cewa, gyare-gyaren da gwamnatin tarayya ta yi a ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, na nuna wasu kyawawan alamu; domin a hankali darajar naira ta ƙaru idan aka kwatanta da kuɗaɗen ƙasashen waje a baya.

Har ila yau, babbar hanyar samun ci gaba ga Nijeriya, a cewarsa; ta ta’allaƙa ne da fannoni daban-daban na tattalin arziƙi, bunƙasa ilimi da sana’o’i, inganta harkokin kiwon lafiya, cibiyoyin tsaro na zamantakewa, samar da ababen more rayuwa da kuma samar da kyakkyawan shugabanci da riƙon amana.

Sannan, ya kuma buƙaci ƴan Nijeriya da su rungumi dabi’ar yin aiki tuƙuru, kana kuma su kasance masu imani, amana, haƙuri da kuma fata na gari.

 

Farfesa
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Next Post
Makonni Biyu Bayan Sace Ɗaliban Makarantar Papiri A Neja, Har Yanzu Babu Tuntuɓa

Makonni Biyu Bayan Sace Ɗaliban Makarantar Papiri A Neja, Har Yanzu Babu Tuntuɓa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.