Mataimakin Shugaban Makarantar Nazarin Tattalin Arziƙi ta Afirka da ke Abuja, Farfesa Mahfouz Adedimeji, ya buƙaci ƴan Nijeriya, musamman matasa da su ɗauki matakan da za su taimaka musu wajen kawar da talauci da kuma taɓarɓarewar tattalin arziƙi.
A cewar mataimakin shugaban, ana kafa gwamnati ne, domin magance buƙatun al’umma, waɗanda a farko suka haɗa da abinci, sutura da kuma matsuguni, wanda dukkaninsu sashe ne tattalin arziƙi.
- Jakadan Sin Ya Gana Da Shugaba Tinubu, Inda Ya Jaddada Alkawarin Sin Na Karfafa Alaka Da Nijeriya
- Sin Ta Baiwa Kauyen Gwaji Na Rage Talauci Na Sin Da Habasha Na’urorin Aikin Noma
Ya ƙara da cewa, idan har aka magance muhimman buƙatu na tattalin arziƙi, babu shakka za a iya shawo kan ƙalubale da dama wanda miliyoyin mutane ke fuskanta, inda ya ƙara da cewa; wannan falsafar ta ɗauki nauyin shigar da ilimin tattalin arziƙi a matsayin ginshiƙin horas da ɗalibai, ba tare da la’akari da nau’o’insu ba. Shugaban ya bayyana wannan tsari a matsayin ilimin da ke keɓe a jami’a.
Yayin da yake bayyana mummunan talauci a matsayin wanni nau’i na rashin ilimi da cikakkiyar lafiya, rashin isasshiyar rayuwa da rashin samun damar yin amfani da kayan amfani na yau da kullum, Farfesa Adedimeji ya ce; guje wa talauci ga mutane, musamman matasa na buƙatar haɓaka aiki ta hanyar ilimi, samar da samfurorin kasuwa da kuma samun basirar da ke haifar da samun kuɗin shiga ko yin aikin da za a biya mutum kuɗi.
Don, wanda ƙwararre ne a fannin ilmin kimiyya ta duniya, kuma jami’in hukumar kula da hada-hadar kuɗi ta Nijeriya, ya kuma jaddada cewa; rage kashe kuɗaɗe da kuma ƙara yawan kuɗaɗen shiga, dabaru ne guda biyu da aka gwada lokaci bayan lokaci na shawo kan matsalar tattalin arziƙi tare da ƙarfafa wa matasa gwiwa, wajen koyon dabi’ar sa kai, domin yana daga cikin samun ƙwarewa da kuma jawo hankalin masu zuwa a nan gaba.
Farfesa Adedimeji ya gabatar da cewa, gyare-gyaren da gwamnatin tarayya ta yi a ƙarƙashin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, na nuna wasu kyawawan alamu; domin a hankali darajar naira ta ƙaru idan aka kwatanta da kuɗaɗen ƙasashen waje a baya.
Har ila yau, babbar hanyar samun ci gaba ga Nijeriya, a cewarsa; ta ta’allaƙa ne da fannoni daban-daban na tattalin arziƙi, bunƙasa ilimi da sana’o’i, inganta harkokin kiwon lafiya, cibiyoyin tsaro na zamantakewa, samar da ababen more rayuwa da kuma samar da kyakkyawan shugabanci da riƙon amana.
Sannan, ya kuma buƙaci ƴan Nijeriya da su rungumi dabi’ar yin aiki tuƙuru, kana kuma su kasance masu imani, amana, haƙuri da kuma fata na gari.














