Gwamnatin Jihar Legas ta kwashe ɗalibai ƴan asalin Jihar fiye da 230 waɗanda suke karatu a Jami’ar Jos, wannan kuwa ya biyo bayan matsalar tsaron da ake fusknata a Jihar Filato, wanda hakak ne ne yasa ka rufe jami’ar da duk wasu harkokin karatu.
A na shi ƙarin haske, Gwamnan Jihar Babajide Sanwo-Olu,ta hanyar ma’aikatar ilimi mai zurfi, ya sa aka samar da motoci waɗanda jami’an tsaro suka rako ɗaliban da abin ya shafa har zuwa Legas ba tare da wata matsala ba.
- NDLEA Ta Bankaɗo Hodar Ibilis Da Aka Ɓoye A Cikin Gwangwanin Kwakwar Manja A Legas
- Payday Loans In Marion Waupaca County Wi Online 24
Hakan na ƙunshe ne a wani jawabin da aka fitar mai ɗauke da sa hannun darekatan al’amuran da suk shafi al’umma, Mamud Hassan.
Hassan ya bayyana Kwamishinan ilimi mai zurfi ne, Tolani Sule, wanda ya amshi ɗalibai waɗanda aka dawo da su gida Legas ya bayyana cewar kwaso su ɗin ya zama dole ne domin, a kare rayuwar al’ummar Jihar Legas waɗanda su ba a gidaba bane suke karatu.
Ya ƙara da cewa gwamnati ba za ta yi biris da rahoton matsalar tsaro a Jos ba ta kuma jinjinawa jami’an tsaro saboda tabbatar da dawowar da ɗaliban lafiya.
Ga bayanin kamar yadda yake, “Zaman lafiya da jindaɗin al’ummar mau shi ne abin karewa, musamman ma matasa waɗanda suke nemn ilimi a faɗin tarayyar Nijeriya, shi ne babban abinda aka fi bamuhimmanci a wannan mulkin.
“Ba za mu kasance daban ba dangane da lamarin rahotannin da suke zuwa daga Jos.Mun godewa Shugaban ƙasa saboda dawo da zaman lafiya a Jihar Filato, gwamnatin Jiha , hukumomin tsaro saboda haɗin kan da suka bada wajen tabbatar da an samu damar fitar da ɗaliban daga wuraren da matsalar ta fi ƙamari , ba tare da wani matsala ba.
“Shi ma a na shi jawabin Babban Sakatare na ma’aikatar ilimi mai zurfi, Adeniran Kasali ya yi kira da ɗalibai su kasance ma su haƙuri. Kamar yadda ya ce, dukkan ɗaliban da suka dawo an duba lafiyarsu lokacin da suka iso Legas kafin a sada su da Iyayensu.
“ Gwamnatin Jihar Legas za ta ci gaba da sa ido kan irin ci gaban da aka samu a Jihar Filato da kuma Jami’a domin a samun sanin irin matakin da za a ɗauka matuƙar zaman lafiya ya dawo kamar yadda kowa ya ke buƙata .
“Babban mai ba gwamna shawara akan manyan makarantu Samuel Kappoa harkokin ɗalibai, Mista Samuel Kappo shi ne ya jago shi ne ya jagoranci dawo da ɗaliban.













Discussion about this post