Duba da yadda farashin Irin Citta ya yi tashin gwaron zabi a wannan shekarar, inda farashin duk buhu guda, mai nauyin kilo 110, ya kai kimanin naira 550,000, wanda hakan yasa mafi akasarin masu yin nomanta za su ragu matuka a kakar noman bana.
Bisa wani bincike da aka gudanar a wasu kasuwannin da ake sayar da cittar, musamman a Jihar Kaduna, ya nuna cewa; manoman nata na ci gaba da nuna damuwa, sakamakon tashin gwauron zabin farashin Irin nata, musamman yayin da suke kan shirye-shiryen tunkarar fara shuka ta.
Idan za a iya tunawa, tun bayan bullar wata cuta da ke lalata cittar da aka shuka a wasu jihohin da ke kasar nan, musamman a shekarar 2024, fannin ke ci gaba da fuskantar gagarumin kalubale.
Kazalika, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta samar da dauki bayan bullar cutar, amma duk da haka; lamarin na ci gaba da jawo hauhawar farashinta.
Wani manomin cittar a Karamar Hukumar Kachia da ke Jihar Kaduna, John S. Hatan, ya sanar da cewa; a 2026, farashin Irin cittar, ya yi matukar tsada, bayan bullar cutar a yankin, inda hakan ya tilasta manomanta, suka rage yawan yadda suka saba nomawa.
A cewarsa, sakamakon wannan matsalar, har yanzu akasarin manoman, sun kasa farfadowa daga asarar da suka tabka.
Ya kara da cewa, kafin bullar cutar, akasarin manomanta a yankin suna yin nomanta, amma yanzu ‘yan kadan daga cikinsu ne ke iya sayen Irinta, saboda tsadar farashin Irin, inda a yanzu ake sayar da duk buhu daya kan kimanin naira 550,000.
Ya ci gaba da cewa, kafin tashin farashin Irin, wasu manoman a yankn, na sayen kimanin buhunhunan Irin har 1,000, domin shukawa a gonakinsu.
A cewarsa, har yanzu, babu wani dauki na tallafi da suka samu daga wurin gwamnati, bayan bullar cutar, inda ya yi kira ga gwamnatin, da ta kawo musu dauki, musamman domin su farfado daga cikin asarar da suka yi, bayan bullar cutar.
Shi ma wani manominta a garin na Kachia, Ibrahim Shagbo, ya sanar da cewa; tsadar farashin Irin, ya hana manomanta da dama fara yin shuka.
Ya kara da cewa, a mako biyu da suka gabata, ana sayar da duk buhu daya na Irinta, kan naira 450,000, inda yanzu farashin ya karu zuwa naira 550,000, kan duk buhu daya.
Shi kuwa, Shu’aibu Isah Marjere, wani manominta a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa; Irin ya yi matukar tsada a 2026, inda hakan, ya tilasta wasu manomanta fara shirin noma wani amfanin gonar daban.
Farashin Buhu Na Irin Citta Ya Kai Naira 550,000 A Kaduna – Manoma
Duba da yadda farashin Irin Citta ya yi tashin gwaron zabi a wannan shekarar, inda farashin duk buhu guda, mai nauyin kilo 110, ya kai kimanin naira 550,000, wanda hakan yasa mafi akasarin masu yin nomanta za su ragu matuka a kakar noman bana.
Bisa wani bincike da aka gudanar a wasu kasuwannin da ake sayar da cittar, musamman a Jihar Kaduna, ya nuna cewa; manoman nata na ci gaba da nuna damuwa, sakamakon tashin gwauron zabin farashin Irin nata, musamman yayin da suke kan shirye-shiryen tunkarar fara shuka ta.
Idan za a iya tunawa, tun bayan bullar wata cuta da ke lalata cittar da aka shuka a wasu jihohin da ke kasar nan, musamman a shekarar 2024, fannin ke ci gaba da fuskantar gagarumin kalubale.
Kazalika, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta samar da dauki bayan bullar cutar, amma duk da haka; lamarin na ci gaba da jawo hauhawar farashinta.
Wani manomin cittar a Karamar Hukumar Kachia da ke Jihar Kaduna, John S. Hatan, ya sanar da cewa; a 2026, farashin Irin cittar, ya yi matukar tsada, bayan bullar cutar a yankin, inda hakan ya tilasta manomanta, suka rage yawan yadda suka saba nomawa.
A cewarsa, sakamakon wannan matsalar, har yanzu akasarin manoman, sun kasa farfadowa daga asarar da suka tabka.
Ya kara da cewa, kafin bullar cutar, akasarin manomanta a yankin suna yin nomanta, amma yanzu ‘yan kadan daga cikinsu ne ke iya sayen Irinta, saboda tsadar farashin Irin, inda a yanzu ake sayar da duk buhu daya kan kimanin naira 550,000.
Ya ci gaba da cewa, kafin tashin farashin Irin, wasu manoman a yankn, na sayen kimanin buhunhunan Irin har 1,000, domin shukawa a gonakinsu.
A cewarsa, har yanzu, babu wani dauki na tallafi da suka samu daga wurin gwamnati, bayan bullar cutar, inda ya yi kira ga gwamnatin, da ta kawo musu dauki, musamman domin su farfado daga cikin asarar da suka yi, bayan bullar cutar.
Shi ma wani manominta a garin na Kachia, Ibrahim Shagbo, ya sanar da cewa; tsadar farashin Irin, ya hana manomanta da dama fara yin shuka.
Ya kara da cewa, a mako biyu da suka gabata, ana sayar da duk buhu daya na Irinta, kan naira 450,000, inda yanzu farashin ya karu zuwa naira 550,000, kan duk buhu daya.
Shi kuwa, Shu’aibu Isah Marjere, wani manominta a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa; Irin ya yi matukar tsada a 2026, inda hakan, ya tilasta wasu manomanta fara shirin noma wani amfanin gonar daban.















Discussion about this post