ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Buhu Na Irin Citta Ya Kai Naira 550,000 A Kaduna – Manoma

by Abubakar Abba
3 weeks ago
Citta

Duba da yadda farashin Irin Citta ya yi tashin gwaron zabi a wannan shekarar, inda farashin duk buhu guda, mai nauyin kilo 110, ya kai kimanin naira 550,000, wanda hakan yasa mafi akasarin masu yin nomanta za su ragu matuka a kakar noman bana.

Bisa wani bincike da aka gudanar a wasu kasuwannin da ake sayar da cittar, musamman a Jihar Kaduna, ya nuna cewa; manoman nata na ci gaba da nuna damuwa, sakamakon tashin gwauron zabin farashin Irin nata, musamman yayin da suke kan shirye-shiryen tunkarar fara shuka ta.

Idan za a iya tunawa, tun bayan bullar wata cuta da ke lalata cittar da aka shuka a wasu jihohin da ke kasar nan, musamman a shekarar 2024, fannin ke ci gaba da fuskantar gagarumin kalubale.

ADVERTISEMENT

Kazalika, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta samar da dauki bayan bullar cutar, amma duk da haka; lamarin na ci gaba da jawo hauhawar farashinta.

Wani manomin cittar a Karamar Hukumar Kachia da ke Jihar Kaduna, John S. Hatan, ya sanar da cewa; a 2026, farashin Irin cittar, ya yi matukar tsada, bayan bullar cutar a yankin, inda hakan ya tilasta manomanta, suka rage yawan yadda suka saba nomawa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

A cewarsa, sakamakon wannan matsalar, har yanzu akasarin manoman, sun kasa farfadowa daga asarar da suka tabka.

Ya kara da cewa, kafin bullar cutar, akasarin manomanta a yankin suna yin nomanta, amma yanzu ‘yan kadan daga cikinsu ne ke iya sayen Irinta, saboda tsadar farashin Irin, inda a yanzu ake sayar da duk buhu daya kan kimanin naira 550,000.

Ya ci gaba da cewa, kafin tashin farashin Irin, wasu manoman a yankn, na sayen kimanin buhunhunan Irin har 1,000, domin shukawa a gonakinsu.

A cewarsa, har yanzu, babu wani dauki na tallafi da suka samu daga wurin gwamnati, bayan bullar cutar, inda ya yi kira ga gwamnatin, da ta kawo musu dauki, musamman domin su farfado daga cikin asarar da suka yi, bayan bullar cutar.

Shi ma wani manominta a garin na Kachia, Ibrahim Shagbo, ya sanar da cewa;  tsadar farashin Irin, ya hana manomanta da dama fara yin shuka.

Ya kara da cewa, a mako biyu da suka gabata, ana sayar da duk buhu daya na Irinta, kan naira 450,000, inda yanzu farashin ya karu zuwa naira 550,000, kan duk buhu daya.

Shi kuwa, Shu’aibu Isah Marjere, wani manominta a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa; Irin ya yi matukar tsada a 2026, inda hakan, ya tilasta wasu manomanta fara shirin noma wani amfanin gonar daban.

Farashin Buhu Na Irin Citta Ya Kai Naira 550,000 A Kaduna – Manoma

Duba da yadda farashin Irin Citta ya yi tashin gwaron zabi a wannan shekarar, inda farashin duk buhu guda, mai nauyin kilo 110, ya kai kimanin naira 550,000, wanda hakan yasa mafi akasarin masu yin nomanta za su ragu matuka a kakar noman bana.

Bisa wani bincike da aka gudanar a wasu kasuwannin da ake sayar da cittar, musamman a Jihar Kaduna, ya nuna cewa; manoman nata na ci gaba da nuna damuwa, sakamakon tashin gwauron zabin farashin Irin nata, musamman yayin da suke kan shirye-shiryen tunkarar fara shuka ta.

Idan za a iya tunawa, tun bayan bullar wata cuta da ke lalata cittar da aka shuka a wasu jihohin da ke kasar nan, musamman a shekarar 2024, fannin ke ci gaba da fuskantar gagarumin kalubale.

Kazalika, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta samar da dauki bayan bullar cutar, amma duk da haka; lamarin na ci gaba da jawo hauhawar farashinta.

Wani manomin cittar a Karamar Hukumar Kachia da ke Jihar Kaduna, John S. Hatan, ya sanar da cewa; a 2026, farashin Irin cittar, ya yi matukar tsada, bayan bullar cutar a yankin, inda hakan ya tilasta manomanta, suka rage yawan yadda suka saba nomawa.

A cewarsa, sakamakon wannan matsalar, har yanzu akasarin manoman, sun kasa farfadowa daga asarar da suka tabka.

Ya kara da cewa, kafin bullar cutar, akasarin manomanta a yankin suna yin nomanta, amma yanzu ‘yan kadan daga cikinsu ne ke iya sayen Irinta, saboda tsadar farashin Irin, inda a yanzu ake sayar da duk buhu daya kan kimanin naira 550,000.

Ya ci gaba da cewa, kafin tashin farashin Irin, wasu manoman a yankn, na sayen kimanin buhunhunan Irin har 1,000, domin shukawa a gonakinsu.

A cewarsa, har yanzu, babu wani dauki na tallafi da suka samu daga wurin gwamnati, bayan bullar cutar, inda ya yi kira ga gwamnatin, da ta kawo musu dauki, musamman domin su farfado daga cikin asarar da suka yi, bayan bullar cutar.

Shi ma wani manominta a garin na Kachia, Ibrahim Shagbo, ya sanar da cewa;  tsadar farashin Irin, ya hana manomanta da dama fara yin shuka.

Ya kara da cewa, a mako biyu da suka gabata, ana sayar da duk buhu daya na Irinta, kan naira 450,000, inda yanzu farashin ya karu zuwa naira 550,000, kan duk buhu daya.

Shi kuwa, Shu’aibu Isah Marjere, wani manominta a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa; Irin ya yi matukar tsada a 2026, inda hakan, ya tilasta wasu manomanta fara shirin noma wani amfanin gonar daban.

Citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Kafa Tarihi, Yayin Da Aka Fara Jigilar Alhazai Daga Filin Jirgin Sama Na Gusau

Gwamna Lawal Ya Kafa Tarihi, Yayin Da Aka Fara Jigilar Alhazai Daga Filin Jirgin Sama Na Gusau

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.