ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Buhu Na Irin Citta Ya Kai Naira 550,000 A Kaduna – Manoma

by Abubakar Abba
2 months ago
Citta

Duba da yadda farashin Irin Citta ya yi tashin gwaron zabi a wannan shekarar, inda farashin duk buhu guda, mai nauyin kilo 110, ya kai kimanin naira 550,000, wanda hakan yasa mafi akasarin masu yin nomanta za su ragu matuka a kakar noman bana.

Bisa wani bincike da aka gudanar a wasu kasuwannin da ake sayar da cittar, musamman a Jihar Kaduna, ya nuna cewa; manoman nata na ci gaba da nuna damuwa, sakamakon tashin gwauron zabin farashin Irin nata, musamman yayin da suke kan shirye-shiryen tunkarar fara shuka ta.

Idan za a iya tunawa, tun bayan bullar wata cuta da ke lalata cittar da aka shuka a wasu jihohin da ke kasar nan, musamman a shekarar 2024, fannin ke ci gaba da fuskantar gagarumin kalubale.

ADVERTISEMENT

Kazalika, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta samar da dauki bayan bullar cutar, amma duk da haka; lamarin na ci gaba da jawo hauhawar farashinta.

Wani manomin cittar a Karamar Hukumar Kachia da ke Jihar Kaduna, John S. Hatan, ya sanar da cewa; a 2026, farashin Irin cittar, ya yi matukar tsada, bayan bullar cutar a yankin, inda hakan ya tilasta manomanta, suka rage yawan yadda suka saba nomawa.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

A cewarsa, sakamakon wannan matsalar, har yanzu akasarin manoman, sun kasa farfadowa daga asarar da suka tabka.

Ya kara da cewa, kafin bullar cutar, akasarin manomanta a yankin suna yin nomanta, amma yanzu ‘yan kadan daga cikinsu ne ke iya sayen Irinta, saboda tsadar farashin Irin, inda a yanzu ake sayar da duk buhu daya kan kimanin naira 550,000.

Ya ci gaba da cewa, kafin tashin farashin Irin, wasu manoman a yankn, na sayen kimanin buhunhunan Irin har 1,000, domin shukawa a gonakinsu.

A cewarsa, har yanzu, babu wani dauki na tallafi da suka samu daga wurin gwamnati, bayan bullar cutar, inda ya yi kira ga gwamnatin, da ta kawo musu dauki, musamman domin su farfado daga cikin asarar da suka yi, bayan bullar cutar.

Shi ma wani manominta a garin na Kachia, Ibrahim Shagbo, ya sanar da cewa;  tsadar farashin Irin, ya hana manomanta da dama fara yin shuka.

Ya kara da cewa, a mako biyu da suka gabata, ana sayar da duk buhu daya na Irinta, kan naira 450,000, inda yanzu farashin ya karu zuwa naira 550,000, kan duk buhu daya.

Shi kuwa, Shu’aibu Isah Marjere, wani manominta a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa; Irin ya yi matukar tsada a 2026, inda hakan, ya tilasta wasu manomanta fara shirin noma wani amfanin gonar daban.

Farashin Buhu Na Irin Citta Ya Kai Naira 550,000 A Kaduna – Manoma

Duba da yadda farashin Irin Citta ya yi tashin gwaron zabi a wannan shekarar, inda farashin duk buhu guda, mai nauyin kilo 110, ya kai kimanin naira 550,000, wanda hakan yasa mafi akasarin masu yin nomanta za su ragu matuka a kakar noman bana.

Bisa wani bincike da aka gudanar a wasu kasuwannin da ake sayar da cittar, musamman a Jihar Kaduna, ya nuna cewa; manoman nata na ci gaba da nuna damuwa, sakamakon tashin gwauron zabin farashin Irin nata, musamman yayin da suke kan shirye-shiryen tunkarar fara shuka ta.

Idan za a iya tunawa, tun bayan bullar wata cuta da ke lalata cittar da aka shuka a wasu jihohin da ke kasar nan, musamman a shekarar 2024, fannin ke ci gaba da fuskantar gagarumin kalubale.

Kazalika, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta samar da dauki bayan bullar cutar, amma duk da haka; lamarin na ci gaba da jawo hauhawar farashinta.

Wani manomin cittar a Karamar Hukumar Kachia da ke Jihar Kaduna, John S. Hatan, ya sanar da cewa; a 2026, farashin Irin cittar, ya yi matukar tsada, bayan bullar cutar a yankin, inda hakan ya tilasta manomanta, suka rage yawan yadda suka saba nomawa.

A cewarsa, sakamakon wannan matsalar, har yanzu akasarin manoman, sun kasa farfadowa daga asarar da suka tabka.

Ya kara da cewa, kafin bullar cutar, akasarin manomanta a yankin suna yin nomanta, amma yanzu ‘yan kadan daga cikinsu ne ke iya sayen Irinta, saboda tsadar farashin Irin, inda a yanzu ake sayar da duk buhu daya kan kimanin naira 550,000.

Ya ci gaba da cewa, kafin tashin farashin Irin, wasu manoman a yankn, na sayen kimanin buhunhunan Irin har 1,000, domin shukawa a gonakinsu.

A cewarsa, har yanzu, babu wani dauki na tallafi da suka samu daga wurin gwamnati, bayan bullar cutar, inda ya yi kira ga gwamnatin, da ta kawo musu dauki, musamman domin su farfado daga cikin asarar da suka yi, bayan bullar cutar.

Shi ma wani manominta a garin na Kachia, Ibrahim Shagbo, ya sanar da cewa;  tsadar farashin Irin, ya hana manomanta da dama fara yin shuka.

Ya kara da cewa, a mako biyu da suka gabata, ana sayar da duk buhu daya na Irinta, kan naira 450,000, inda yanzu farashin ya karu zuwa naira 550,000, kan duk buhu daya.

Shi kuwa, Shu’aibu Isah Marjere, wani manominta a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa; Irin ya yi matukar tsada a 2026, inda hakan, ya tilasta wasu manomanta fara shirin noma wani amfanin gonar daban.

Citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Kafa Tarihi, Yayin Da Aka Fara Jigilar Alhazai Daga Filin Jirgin Sama Na Gusau

Gwamna Lawal Ya Kafa Tarihi, Yayin Da Aka Fara Jigilar Alhazai Daga Filin Jirgin Sama Na Gusau

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.