ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Buhu Na Irin Citta Ya Kai Naira 550,000 A Kaduna – Manoma

by Abubakar Abba
1 month ago
Citta

Duba da yadda farashin Irin Citta ya yi tashin gwaron zabi a wannan shekarar, inda farashin duk buhu guda, mai nauyin kilo 110, ya kai kimanin naira 550,000, wanda hakan yasa mafi akasarin masu yin nomanta za su ragu matuka a kakar noman bana.

Bisa wani bincike da aka gudanar a wasu kasuwannin da ake sayar da cittar, musamman a Jihar Kaduna, ya nuna cewa; manoman nata na ci gaba da nuna damuwa, sakamakon tashin gwauron zabin farashin Irin nata, musamman yayin da suke kan shirye-shiryen tunkarar fara shuka ta.

Idan za a iya tunawa, tun bayan bullar wata cuta da ke lalata cittar da aka shuka a wasu jihohin da ke kasar nan, musamman a shekarar 2024, fannin ke ci gaba da fuskantar gagarumin kalubale.

ADVERTISEMENT

Kazalika, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta samar da dauki bayan bullar cutar, amma duk da haka; lamarin na ci gaba da jawo hauhawar farashinta.

Wani manomin cittar a Karamar Hukumar Kachia da ke Jihar Kaduna, John S. Hatan, ya sanar da cewa; a 2026, farashin Irin cittar, ya yi matukar tsada, bayan bullar cutar a yankin, inda hakan ya tilasta manomanta, suka rage yawan yadda suka saba nomawa.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

A cewarsa, sakamakon wannan matsalar, har yanzu akasarin manoman, sun kasa farfadowa daga asarar da suka tabka.

Ya kara da cewa, kafin bullar cutar, akasarin manomanta a yankin suna yin nomanta, amma yanzu ‘yan kadan daga cikinsu ne ke iya sayen Irinta, saboda tsadar farashin Irin, inda a yanzu ake sayar da duk buhu daya kan kimanin naira 550,000.

Ya ci gaba da cewa, kafin tashin farashin Irin, wasu manoman a yankn, na sayen kimanin buhunhunan Irin har 1,000, domin shukawa a gonakinsu.

A cewarsa, har yanzu, babu wani dauki na tallafi da suka samu daga wurin gwamnati, bayan bullar cutar, inda ya yi kira ga gwamnatin, da ta kawo musu dauki, musamman domin su farfado daga cikin asarar da suka yi, bayan bullar cutar.

Shi ma wani manominta a garin na Kachia, Ibrahim Shagbo, ya sanar da cewa;  tsadar farashin Irin, ya hana manomanta da dama fara yin shuka.

Ya kara da cewa, a mako biyu da suka gabata, ana sayar da duk buhu daya na Irinta, kan naira 450,000, inda yanzu farashin ya karu zuwa naira 550,000, kan duk buhu daya.

Shi kuwa, Shu’aibu Isah Marjere, wani manominta a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa; Irin ya yi matukar tsada a 2026, inda hakan, ya tilasta wasu manomanta fara shirin noma wani amfanin gonar daban.

Farashin Buhu Na Irin Citta Ya Kai Naira 550,000 A Kaduna – Manoma

Duba da yadda farashin Irin Citta ya yi tashin gwaron zabi a wannan shekarar, inda farashin duk buhu guda, mai nauyin kilo 110, ya kai kimanin naira 550,000, wanda hakan yasa mafi akasarin masu yin nomanta za su ragu matuka a kakar noman bana.

Bisa wani bincike da aka gudanar a wasu kasuwannin da ake sayar da cittar, musamman a Jihar Kaduna, ya nuna cewa; manoman nata na ci gaba da nuna damuwa, sakamakon tashin gwauron zabin farashin Irin nata, musamman yayin da suke kan shirye-shiryen tunkarar fara shuka ta.

Idan za a iya tunawa, tun bayan bullar wata cuta da ke lalata cittar da aka shuka a wasu jihohin da ke kasar nan, musamman a shekarar 2024, fannin ke ci gaba da fuskantar gagarumin kalubale.

Kazalika, gwamnatin tarayya ta shelanta cewa; ta samar da dauki bayan bullar cutar, amma duk da haka; lamarin na ci gaba da jawo hauhawar farashinta.

Wani manomin cittar a Karamar Hukumar Kachia da ke Jihar Kaduna, John S. Hatan, ya sanar da cewa; a 2026, farashin Irin cittar, ya yi matukar tsada, bayan bullar cutar a yankin, inda hakan ya tilasta manomanta, suka rage yawan yadda suka saba nomawa.

A cewarsa, sakamakon wannan matsalar, har yanzu akasarin manoman, sun kasa farfadowa daga asarar da suka tabka.

Ya kara da cewa, kafin bullar cutar, akasarin manomanta a yankin suna yin nomanta, amma yanzu ‘yan kadan daga cikinsu ne ke iya sayen Irinta, saboda tsadar farashin Irin, inda a yanzu ake sayar da duk buhu daya kan kimanin naira 550,000.

Ya ci gaba da cewa, kafin tashin farashin Irin, wasu manoman a yankn, na sayen kimanin buhunhunan Irin har 1,000, domin shukawa a gonakinsu.

A cewarsa, har yanzu, babu wani dauki na tallafi da suka samu daga wurin gwamnati, bayan bullar cutar, inda ya yi kira ga gwamnatin, da ta kawo musu dauki, musamman domin su farfado daga cikin asarar da suka yi, bayan bullar cutar.

Shi ma wani manominta a garin na Kachia, Ibrahim Shagbo, ya sanar da cewa;  tsadar farashin Irin, ya hana manomanta da dama fara yin shuka.

Ya kara da cewa, a mako biyu da suka gabata, ana sayar da duk buhu daya na Irinta, kan naira 450,000, inda yanzu farashin ya karu zuwa naira 550,000, kan duk buhu daya.

Shi kuwa, Shu’aibu Isah Marjere, wani manominta a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna ya bayyana cewa; Irin ya yi matukar tsada a 2026, inda hakan, ya tilasta wasu manomanta fara shirin noma wani amfanin gonar daban.

Citta
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Kafa Tarihi, Yayin Da Aka Fara Jigilar Alhazai Daga Filin Jirgin Sama Na Gusau

Gwamna Lawal Ya Kafa Tarihi, Yayin Da Aka Fara Jigilar Alhazai Daga Filin Jirgin Sama Na Gusau

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.