ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kakakin Majalisa Ga Tinubu: Ka Dauki Kwararan Matakai Kan Karuwar Matsalolin Tsaro

by Khalid Idris Doya
3 years ago
kakakin majalisa

Kakakin Majalisar Wakilai ta Tarayya, Tajudeen Abbas, ya bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da ya rufe idonsa ya dauki kwararan matakai kan mukarrabansa da suka kasa gudanar da ayyukan da ke wuyayensu.

Ya ce, ta hanyar fitar da wadanda suka kasa kokari daga cikin hadiman shugaban kasa za a samu natija a yaki da ake yi kan matsalolin tsaro a fadin kasar nan.

  • Bikin Al’adun Gargajiya Na Rigata Karo na 3 Zai Gudana A 8 Ga Fabrairu A Yauri
  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Kai Don Ciyar Da Jihar Gaba

Ya kuma ba da shawarar cewa a bullo da wasu sabbin dabarun hikima wajen tunkarar matsalolin tsaro da suka addabi kasar nan ta Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Abbas ya yi wannan kiran ne a ranar Talata yayin da majalisar ta dawo hutun da ta tafi na bukukuwan kirsimeti da na sabuwar shekara.

Da yake kokawa kan karuwar matsalolin tsaro a Nijeriya wanda har kana samu salwantuwan rayukan ‘yan Nijeriya da daman gaske a ‘yan kwanakin baya a jihohin Filato, Kaduna da wasu sassan kasar, Abbas ya lura kan cewa, muddin ba a tashi tsaye aka kawo karshen matsalolin ba, nan gaba matsalar tsaro zai zama babban barazana ga daurewar kwanciyar hankalin kasar.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ya ce, “Duk da daukan matakan tsaro daban-daban, amma har yanzu kalubalen matsalar tsaro na ci gaba da addabar jama’a, muna sako-sako da kokarinmu da matakin da muke dauka na shawo kan matsalolin da ke barazana ga daurewar zaman lafiya da kwanciyar hankali hadi da ci gaban kasarmu.

“Akwai bukatar mu tunatar da kanmu cewa dabarun tsaro da ake bi na tsawon lokaci ba su wadatar da mu ba. Don haka, lokaci ya yi da za a zauna a sake tunani a fito da wasu muhimman dabarbarun da za a dauka da kuma tsare-tsaren da za su taimaka wajen kawo karshen matsalolin tsaro da suke addabarmu.

“Ga kuma jaruman jami’anmu na tsaro, a yayin da muke jinjina wa kokarinku da sadaukarwarku, lokaci ya yi kuma da za ku sake waiwayar hanyoyi da dabarbarun da kuke bi domin ingantasu da sabuntasu. Makiya na sauya taku, dole ne muma mu yi hakan. Na kalubalanceku a kan wannan da cewar ku tashi tsaye wajen sauke nauyin da ke kawukanku na kare mana jama’a da dukiyarsu.”

Ya ce, a matsayinsa na dan kasa da ya damu kuma lamarin ya shafa, matsalar tsaro ya dameshi kuma na daga cikin abubuwan da suka tsaya masa a wuya da sauran al’umman kasa.

kakakin majalisa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Yadda Sabon Rikicin ECOWAS Zai Shafi Nijeriya

Yadda Sabon Rikicin ECOWAS Zai Shafi Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.