ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashe-Kashe A Arewa: Gamayyar Kungiyoyi Sun Yi Zargin Akwai Hannun Kasashen Waje

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
4 months ago
Arewa

Gamayyar Kungiyoyin Arewa (CNG) ta nuna damuwa kan yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara a Arewacin Nijeriya, tare da gargadin kada a yi amfani da bambancin kabilanci da addini, da kuma shigar wasu ‘yan waje cikin rikice-rikicen.

Kungiyar ta yi Allah-wadai da hare-haren baya-bayan nan a jihohin Filato da Jihar Kaduna, tana mai bayyana su a matsayin mugwaye kuma marasa imani.

  • Jakadan Sin a Najeriya Ya Gana Da Shugaban Kwamitin Kula Da Makarantun Noma Da Cibiyoyin Bincike Na Majalisar Dattawa Ta Najeriya
  • Kasar Sin Ta Dakile Matsalar Safarar Yara Da Mata 

Ta ambaci kashe mutane akalla 14 a Anguwan Rukuba, Karamar Hukumar Jos ta Arewa, da kuma wani hari a wurin biki a Karamar Hukumar Kagarko ta Kaduna, inda aka kashe mutane 13 tare da sace wasu da dama.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da mai kula da harkokin kungiyar na kasa, Jamilu Aliyu Charanchi ya fitar, ya ce kai hare-hare kan fararen hula babban laifi ne ga bil’adama, kuma dole ne kowa ya yi Allah-wadai da hakan.

Kungiyar ta kuma nuna damuwa kan rahotannin ramuwar gayya da wasu matasa ke yi a Jihar Filato, tana gargadin cewa: Ramuwar gayya da tashin hankali na jama’a na iya kara rura wutar rikici. Ware mutane bisa asali ko addini zai kara rarrabuwar kai. Irin wadannan matakai suna taimaka wa masu neman tayar da fitina

LABARAI MASU NASABA

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Charanchi ya bukaci shugabannin addini, dattawa da masu tasiri a al’umma da su yi taka-tsantsan, su guji furta kalaman da za su kara dagula al’amura.

Kungiyar ta kuma yi gargadi kan rawar da wasu ‘yan waje da kungiyoyi marasa tushe ke takawa, tana zargin cewa suna amfani da rikice-rikicen cikin gida domin cimma manufofinsu na tayar da zaune tsaye.

Ta kuma yi kira ga gwamnatocin tarayya da na jihohi da su: Dauki matakan gaggawa wajen kare rayuka da dukiyoyi. Inganta hanyoyin tattara bayanan sirri da kuma martani ga hare-hare. Samar da tsare-tsare na dindindin da za su magance tushen matsalar tsaro.

Haka kuma, ta bukaci hukumomin tsaro su tabbatar da kamo masu aikata laifuka tare da gurfanar da su a gaban shari’a, domin dawo da amincewar jama’a.

CNG ta jajanta wa iyalan wadanda suka rasa rayukansu, tare da kira ga al’umma da su kasance masu natsuwa, bin doka, da kuma hadin kai domin gujewa fadawa cikin rikicin da zai iya raba kan jama’a.

Arewa
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai
Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

MASU ALAKA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Arewa
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa
Manyan Labarai

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Next Post
Daga Ƙarshe, Tinubu Ya Naɗa Jakadu Uku Bayan Tsawon Shekara 2 Ana Jira

2027: Batun Murabus Din Masu Rike Da Mukaman Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Arewa

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Arewa

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Arewa

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.