ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Batun Murabus Din Masu Rike Da Mukaman Gwamnati

by Leadership Hausa
4 months ago
Gwamnati

A makon da ya gabata ne, shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci wadanda ya nada, a mukaman siyasa, musamman wadanda, ke da ra’ayin tsayawa takara cewa, su yi murabus a ranar 31 na watan Maris din 2026.

Wannan umarnin na shugaban ya nuna a zahiri cewar, an riga an kada, Gangar tunkarar zaben kakar 2027 ke nan.

  • Kasar Sin Ta Dakile Matsalar Safarar Yara Da Mata 
  • Sin Ta Kaddamar Da Shirin “Operation Sky Net 2026” Don Taso Keyar Masu Cin Hanci Da Suka Tsere

Kazalika, umarnin ya kuma cewar, yanzu a kasar, za a iya cewa, an jinge batun gudanar da harkar mulki, zuwa ga maganar tunkarar zaben gama gari, a kasar

ADVERTISEMENT

Wannan lamarin dai, ya jefa damuwa, a zukatan ‘yan  kasar, kan irin ingancin bangaren gudanar da shugabancin da ake gudanar wa a kasar.

A saboda da haka, wannan Jaridar, ta yi tsammanin wannan umarnin na shugaban, zai sanya, musamman, manyan jiga-jigan masu rike da mukaman siyasa a matakin gwamnatin tarayya, za su yi murabus, daga mukaman na su.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Babbar tambayar da ke da matukar sarkakiya kan wannan batun shi ne, shin shugaba Tinubu, zai cike gibin wadannan mukaman na ‘yan siyasar da suka yi murabus ne, ko kuwa, za a bar gurbin da suka bari ne, ba tare da ya nada kowa ba ?

Idan matsalar ta ke shi ne, ko da ma, shugaban ya nada wadanda za su cike gibin na wadanda suka yi murabus saboda rashin sanin makamar aiki a tsakanin su, zai yi matukar wuya, su iya tafiyar da bangaren gudanar da shugabancin, yadda ake bukata, musamman kari da cewa an nada su ne, a kurarren lokaci.

Bugu da kari, a gefe daya kuma, babu wani tabbacin cewa, wata sabuwar gwamnatin da ta lashe zabe, za ta ci gaba da gudanar da shirye-shiyen da tsohuwar gwamnatin da ta gabata, ta faro da su, inda hakan, zai kara haifar da wani sabon rudu, a bangaren gudanar da shugabancin kasar.

Hakazalika, ma’aikatun da kuma hukumomin gwamnati, na taka muhimmiyar rawa wajen wandar da tsare-tsaren gwamnati, gudanar da ayyukan gwamnatin da kuma sanya ido kan tafiyar da tattalin arzikin kasa

Amma, idan har aka samu wani gibi, na masu rike da mukaman na siyasa, tabbas za a samu tsaikon ci gaba da wanzar da daukar matakai a bangaren gudanar da shugabancin,  tare da karya lagon gudanar da sanya ido, kan tafiyar da ayyukan gwamnatin wanda a karshe, hakan zai shafi rayuwar ‘yan kasar

Kazalika, a wani bangaren, wadanda za a nada a mukaman na wucin gadi za su iya mayar da hankali a bangren siyasa kachokam, maimakon, mayar da hankali a bangren gudanar da shugabanci.

A nan, wannan Jaridar na nuna matukar damuwa, musamman kan matsalar da wannan gibin dai haifar.

Ko da yake dai, wannan umarnin na shugaban kasa, ya yi shi ne, daidai da tsarin da kundin mulkin kasar ya tana musamman duba da cewa, an kirkiro da tsarin ne, domin yin adalaci ga sauran wadanda ba su rike da mukaman gwamnati, domin kaucewa, yin amfani da karfin iko,a yayin gudanar da zabuka, a kasar.

Domin a kaucewa matsalar da wannan gibin zai haifar, akwai matukar bukatar, gwamnatin ta samar da matakan da suka kamata.

Misali, daya daga cikin matakan da ya kamata gwamnatin ta dauka shi ne, nada jami’ai a mukaman siyasa na wucin gadi wadanda kuma za su ci gaba da tafiyar da harkar shuganci yadda ya kamata ba kuma tare da, fuskantar wata tangarda ba.

Dole ne kuma a tafiyar da aikin kamar yadda dokar kasa, ta tanada.

A namu tunanin a wannan Jaridar, shawar ita ce, shugaban kasa, mai yuwa ya yi tunanin nada masu sanya ido wajen tafiyar da ma’akatun gwamnatin, mumamman domin ayyukan gwamnatin, su tafi yadda ya kamata.

Duk da cewa, wannan ba wai wani tsari ne da ya kasance a hukumance ba, amma zai iya rage tarnakin da bangaren gudanar da shugabancin kasar zai iya fuskanta dangane da wannan gibin da masu murabus, suka bari.

Hakazalika, a gefe daya kuma, a yanzu dai, fannin tattalin arzikin kasar nan, na kan wani babban siradi

duba da wasu matsaloli na cikin gida ta yake fuskanta, inda kuma, a gefe daya, na yakin da ake ci gaba da gabzawa, a Gabas ta Tsakiyawato, a tsakanin kasashen Iran da Isara’ila da kuma Amurka.

Yakin dai, ya haifar da tashin gwaron Zabi, musamman a fannin makamashi da tsadar man fetur da dangoginsa, a  duniya baki daya ciki har da kasar nan.

Misali, a bangaren kasar nan, lamarin ya kara ta’azzara kuncin tattalin arzikin’ yan kasar,musamman talakawa duba da yadda lamarin ya haifar tashin farashin kayan abinci da tsadar sufuri da sauransu.

A kasa kamar irin Nijeriya wannan batun, ba abu ne da ya ke da wani sauki ko kadan ba, musamman duba da yadda hauhawan farashin kayan abinci a kasar ke dakile magidanta da dama, iya sayawa iyalansu kayan masatufi.

A yanayi irin wannan da kasar ta tsinci kanta a ciki a yanzu,kamata ya yi gwamnatin tarayya ta mayar da hankali, wajen saita fannin tattalin arzikin kasar tare da kuma samar da tsare-tsaren da za su samarwa da talakawan kasar, musamman saukin radadin rayuwar da suke ci gaba da fuskanta.

Nauyi a kan kowacce gwamnati, na ta tabbatar da an mika ragamar shugabanci daga gun wata gwamnatin zuwa wata sabuwar gwamnatin, musamman,domin a ci gaba da gudanar da harkar shuganci.

A nan, za mu iya cewa, ya zama wajibi shugaban kasa ya dauki matakan da suka kamata domin a magance wannan matsalar ta gibin da za ssmu.

Kazalika,’ yan Nijeriya na da hakkin samun shugabanci na gari, tare da kuma samar masu da ababen more rayuwa.

Nijeriya ba za ta iya rungume hannunta a bangaren abinda ya shafi tafiyar da shugabanci ba dole a san, matakan da ya kamata a dauka.

Zabuka dai, suna zuwa ne, suna kuma shudewa, amma harkar tafiyar da shugabanci, abu ne, da ya ke daram dam,wanda kuma za a rinka tafiyar da shi,dai dai da ra’ayin yan kasa.

Gwamnati
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
EFCC Ta Nemi Kotu Ta Ƙwace Kadarori 57 Da Ake Dangantawa Ga Malami

EFCC Ta Nemi Kotu Ta Ƙwace Kadarori 57 Da Ake Dangantawa Ga Malami

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Gwamnati

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Gwamnati

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Gwamnati

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.