ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Shettima

Fadar Shugaban Kasar ta yi Allah wadai da shekaru da dama da aka shafe ana tafka ta’asa da rashin amfani da kadarorin kasar a ciki da wajen iyakokin kasar, lamarin da ke janyo asarar kudaden shiga da ke kawo cikas ga ci gaban tattalin arziki.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ne ya bayyana hakan jiya a wajen taron kula da dukiyar al’umma a Abuja.

  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka
  • Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

Shettima ya ce an kama manyan motoci 45 dauke da masara a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa kasashen makwabta da tsakar daren ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A cikin dare uku da suka wuce, an kama manyan motoci 45 na masara ana jigilar su zuwa kasashe makwabta. Kawai a cikin Kauyen Ilela, akwai hanyoyin fasa kwauri guda 32. Kuma a lokacin da aka kama wadannan kayan abinci, farashin masara ya fadi da Naira 10,000. Wato ana sayar da ita Naira Naira 60,000 ta sakko zuwa Naira 50,000.

“Don haka, akwai wadanda ke da aniyar yi wa al’ummarmu zagon kasa, amma wannan lokaci ne da ya kamata mu hada kai zuwa wata kungiya mai zaman kanta. Dole ne mu tsaya mu yi wa kasa aiki. A yanzu mun wuce batun siyasa, magana ake ta a tsaya a fuskanci gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Abin takaicin shi ne, har yanzu wasu daga cikin ‘yan kasarmu sun tsunduma a cikin salon siyasa. Su ne masu aikata ta’addanci, suna ba da shawarar cewa Najeriya ta bi irin hanyar da Lebanon ke kai. Amma hakan ba za ta yiwu ba, domin Nijeriya ta fi karfin haka, kuma da sannu za a shawo kan lamarin.”

A cewar Shettima, maimakon su jira har zuwa 2027, ‘yan siyasa masu ra’ayin rikau wadanda ba za su iya samun madafun iko ta hanyar katin zabe ba, sun gwammace su jefa kasar nan cikin halin rashin tabbas.

Mataimakin shugaban kasar ya amince cewa ‘yan Nijeriya na fuskantar kalubale, ya kuma bukaci a yi hakuri, domin ya bayyana kwarin gwiwar cewa nan ba da dadewa ba al’amura za su canja.

Shettima, who represented Tinubu at the ebent, hinted at plans by the present administration to create millions of jobs by unlocking the balue of Nigeria’s bast public assets to optimize and double the country’s Gross Domestic Product (GDP).

Shettima, wanda ya wakilci Tinubu a wajen taron, ya yi ishara da tsare-tsare da gwamnati mai ci ke yi na samar da miliyoyin ayyukan yi ta hanyar bude dimbin kadarorin al’ummar Nijeriya don ingantawa tare da ninka arzikin kasa (GDP).

Ya ce tare da farfado da tattalin arziki a matsayin babban abin da ta sa a gaba, gwamnatin tarayya na da burin tara akalla Dala biliyan 10 domin kara kudin musayar kudaden waje wanda hakan kuma zai daidaita darajar Naira.

Ministan kudin ya ba da tabbacin cewa yayin da ake sakin ton 42,000 na hatsi iri-iri tare da ton 60,000 nan gaba kadan, a wani mataki na dakile hauhawar farashin kayan abinci, farashin kayan abinci zai ragu a watanni masu zuwa sakamakon ayyuka da manufofin gwamnati.

An shirya taron ne domin tsara dabarun sarrafa dukiyoyi da albarkatun kasa yadda ya kamata domin inganta jin dadin al’ummarta.

Shettima
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Yadda Zaki Ya Halaka Mai Ba Shi Abinci Har Lahira

Yadda Zaki Ya Halaka Mai Ba Shi Abinci Har Lahira

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.