ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Shettima

Fadar Shugaban Kasar ta yi Allah wadai da shekaru da dama da aka shafe ana tafka ta’asa da rashin amfani da kadarorin kasar a ciki da wajen iyakokin kasar, lamarin da ke janyo asarar kudaden shiga da ke kawo cikas ga ci gaban tattalin arziki.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ne ya bayyana hakan jiya a wajen taron kula da dukiyar al’umma a Abuja.

  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka
  • Mun Hana Kai Wa ‘Yan Bindiga Burodi Ba Hana Sayarwa Ko Gasawa Ba – Dauda

Shettima ya ce an kama manyan motoci 45 dauke da masara a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa kasashen makwabta da tsakar daren ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A cikin dare uku da suka wuce, an kama manyan motoci 45 na masara ana jigilar su zuwa kasashe makwabta. Kawai a cikin Kauyen Ilela, akwai hanyoyin fasa kwauri guda 32. Kuma a lokacin da aka kama wadannan kayan abinci, farashin masara ya fadi da Naira 10,000. Wato ana sayar da ita Naira Naira 60,000 ta sakko zuwa Naira 50,000.

“Don haka, akwai wadanda ke da aniyar yi wa al’ummarmu zagon kasa, amma wannan lokaci ne da ya kamata mu hada kai zuwa wata kungiya mai zaman kanta. Dole ne mu tsaya mu yi wa kasa aiki. A yanzu mun wuce batun siyasa, magana ake ta a tsaya a fuskanci gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

“Abin takaicin shi ne, har yanzu wasu daga cikin ‘yan kasarmu sun tsunduma a cikin salon siyasa. Su ne masu aikata ta’addanci, suna ba da shawarar cewa Najeriya ta bi irin hanyar da Lebanon ke kai. Amma hakan ba za ta yiwu ba, domin Nijeriya ta fi karfin haka, kuma da sannu za a shawo kan lamarin.”

A cewar Shettima, maimakon su jira har zuwa 2027, ‘yan siyasa masu ra’ayin rikau wadanda ba za su iya samun madafun iko ta hanyar katin zabe ba, sun gwammace su jefa kasar nan cikin halin rashin tabbas.

Mataimakin shugaban kasar ya amince cewa ‘yan Nijeriya na fuskantar kalubale, ya kuma bukaci a yi hakuri, domin ya bayyana kwarin gwiwar cewa nan ba da dadewa ba al’amura za su canja.

Shettima, who represented Tinubu at the ebent, hinted at plans by the present administration to create millions of jobs by unlocking the balue of Nigeria’s bast public assets to optimize and double the country’s Gross Domestic Product (GDP).

Shettima, wanda ya wakilci Tinubu a wajen taron, ya yi ishara da tsare-tsare da gwamnati mai ci ke yi na samar da miliyoyin ayyukan yi ta hanyar bude dimbin kadarorin al’ummar Nijeriya don ingantawa tare da ninka arzikin kasa (GDP).

Ya ce tare da farfado da tattalin arziki a matsayin babban abin da ta sa a gaba, gwamnatin tarayya na da burin tara akalla Dala biliyan 10 domin kara kudin musayar kudaden waje wanda hakan kuma zai daidaita darajar Naira.

Ministan kudin ya ba da tabbacin cewa yayin da ake sakin ton 42,000 na hatsi iri-iri tare da ton 60,000 nan gaba kadan, a wani mataki na dakile hauhawar farashin kayan abinci, farashin kayan abinci zai ragu a watanni masu zuwa sakamakon ayyuka da manufofin gwamnati.

An shirya taron ne domin tsara dabarun sarrafa dukiyoyi da albarkatun kasa yadda ya kamata domin inganta jin dadin al’ummarta.

Shettima
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Yadda Zaki Ya Halaka Mai Ba Shi Abinci Har Lahira

Yadda Zaki Ya Halaka Mai Ba Shi Abinci Har Lahira

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.