Shugaban kiristoci na Arewacin Nijeriya (NCA), Rabaran. Joseph John Hayab, ya yi kira da gwamnatin tarayya da cewar ta shigar da lamarin irin addinin da mutum ya ke yi a tambayoyin ƙidayar jama’ar da za ayi ta ƙasa nan gaba,abinda zai sa ayi hakan shi ne domin a gane waɗanne irin ƙungiyoyin addinai ne suke da nasu goyon baya da yawa.
Hayab ya ce rashin haƙiƙanin abubuwan da za a dogara da su yawan magoya bayan addini ya sa ana ta wasu maganganun da basu da wata hujja da take nuna wane addini ne ya fi yawan waɗanda suke goyon bayan shi, domin kuwa irin hakan yana ta sa a riƙa tada jijiyar wuya,ga kuma rashin kwanciyar hankalin da zai iya samar da wani lamarin da zai yi wa al’umma daɗi ba.
Ya yi wannan kiran ne ranar Litinin lokacin shirin gidan Talabijin na Channels mai taken tsokacin safe,domin ya maida martini a maganganun da , Sheikh Sani Yahaya Jingir,ya yi inda yake kare lamarin ƴantakara Shugaban ƙasa musulmi da musulmi, saboda kwai la’akari da yadda yawan musulmi ya ke, da kuma yadda su Musulman suke da kuma yadda aka san su.
Jingir ya yi maganar ne a wani taron da aka shirya wanda ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iƙamatus Sunnah (JIBWIS) ta shirya a Kano, wanda Gwamnoni biyu suka samu halarta na Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf da takwaransa na Jihar Jigawa Jigawa, Umar Namadi.
A wani bidiyon da aka saki daga taron, Shehin ya yi kira da Muslimai su haɗa kansu, ba ma kamar idan suka yi la’akari da yawansu idan suna buƙatar su yi amfani da yawansu domin su samu abinda suke buƙata akan lamarin siyasa, yayin da kuma yake cewar su Kiristocin ai “Kafirai ne.”
Da yake maida na shi martanin dangane da maganganun da Sheikh Jingir ya yi,Hayab ya ce maganganun da aka yi sun ƙara nuna buƙatar da ake da ita ta ƙasar Nijeriya ta samu haƙiƙanin yawan mutanen da suke bin addinai mabambanta, ba kawai ayi ta dogaro da waɗansu abubuwan da ba a tabbatar da gaskiyar lamarin ba.
Shugaban na ƙungiyar Kiristocin da suke daga Arewacin Nijeriya ya yi kira da gwamnatin tarayya ta shigar da lamarin da ya shafi tambayoyi a kan addini a ƙidayar jama’ar da za a yi nan gaba, inda ya ke cewa duk bayanan da aka tattara za su iya nunawa gaskiyar yadda lamarin addinan ƙasa suke.
“Ya dace ayi tambaya game da addini. Mu san gaskiya wanda ya ke a ƙasar nan da kuma ko kashi nama ne suke, daganan mutane za su daina yi ma wasu ƴan Nijeriya maganganun da basu da ce ba kamar yadda Hayab ya ce,”.
Ya ce babu wani addinin da zai yi amfani da ƙarfin yawan magoya bayan sa ya sa magoya bayan addinin su riƙa yi ma wasu maganganun da basu dace ba,ko kuma su yi amfani da hakan domin su samu wani tagomashin siyasa fiye da sauaran ƴan Nijeriya.
Akan matsalar da take shafar takarar Shugaban ƙasa ta Muslim-Muslim wato ɗantakarar Shugaban ƙasa da mataimakin sa, Hayab cewa ya yi abinda ke damun Kiristoci ba wai su hana Musulmai damar da suke da ita, ta taimakawa ɗantakarar da ya ke Musulmi ba, amma dai da buƙatar yin adalci, a riƙa tafiya tare da kuma ganin ƙima/ mutuncin juna.














