ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Ƙare Dangi: Sojojin Amurka Sun Fara Aikin Samar Da Tsaro A Nijeriya

by Sani Anwar and Sulaiman
4 months ago
Amurka

Kimanin jami’an sojan Amurka 100 tare da kayan yakinsu, sun isa filin jirgin saman Bauchi, domin tallafa wa sojojin Nijeriya a fannin horo da taimakon fasaha da kuma hadin gwiwar leken asiri, kamar yadda hedkwatar tsaro ta kasa ta sanar a ranar Litinin.

Daraktan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Samaila Uba, a wata sanarwa da ya fitar ya ce; turo sojojin wani Bangare ne na hadin gwiwar tsaron Nijeriya da Amurka, biyo bayan tattaunawar da aka yi ta hadin gwiwa a kwanan baya tsakanin tawagogin sojojin kasashen biyu.

  • Jerin Sharuddan Da Chelle Ya Gindayawa NFF Domin Cigaba Da Jagorantar Super Eagles 
  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

“Isowar jami’an Amurka, shiri ne na da gangan, bisa ga bukatar da gwamnatin tarayyar Nijeriya ta gabatar na neman tallafi wajen magance bukatu na horar da sojoji,” in ji hedikwatar

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, hadin gwiwar na nufin samar da damammaki na fasaha na musamman, don karfafa karfin Nijeriya na dakile barazanar ‘yan ta’adda da kuma kare al’ummomi masu rauni a fadin kasar.

Manjo Janar Uba ya jaddada cewa, ma’aikatan na Amurka, kwararru ne da ke aiki a fagen bayar da shawara da horarwa, ba sojojin yaki kawai ba ne, sannan kuma za a gudanar da dukkan ayyuka a karkashin iko da shugabanci da kuma kula da gwamnatin Nijeriya tare da hadin gwiwa da rundunar sojojin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Hedikwatar ta kara da cewa, sojojin Nijeriya tare da masu bayar da shawara na Amurka, za su gudanar da atisayen horaswa na hadin gwiwa da tsare-tsaren hadin gwiwa da suka shafi leken asiri, wanda aka tsara domin inganta karfin sojojin da za su iya ganowa tare da dakile kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi da ke neman tada zaune tsaye a kasar.

“Rundunar Sojin Nijeriya na ci gaba da dagewa wajen yakar kungiyoyin ‘yan ta’adda da ke barazana ga daukacin tsaron kasa ‘yan kasar,” in ji sanarwar, tare da tabbatar wa ‘yan Nijeriya gaskiya da kuma bayanan da suka dace game da hadin gwiwar.

Trump ya ce, za a iya samun karin matakan sojan Amurka a Nijeriya, yayin da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa; tun a karshen watan Nuwamba ne, Amurka ta fara gudanar da zirga-zirgar jiragen sama a kasar daga Ghana.

 

Kisan Kare Dangi Na Kirista

Dangantaka tsakanin Nijeriya da Amurka ta sauya, bayan da Trump ya yi barazanar shiga Nijeriya a karshen shekarar da ta gabata, domin daukar fansar abin da ya kira da ‘kisan kare dangi na Kiristoci’.

Bayan ‘yan makwanni, a ranar Kirsimeti, jiragen ruwan yakin sojojin ruwan Amurka tare da taimakon jami’an leken asirin Nijeriya, sun harba makamai masu linzami na Tomahawk guda 16, a wani abin da Trump ya ce; ‘yan ta’adda ne ke da alhakin kashe Kiristocin Nijeriya.

Nijeriya dai, ta fuskanci matsanancin matsin lamba daga Amurka, a kan ta dauki mataki bayan Trump ya yi zargin cewa; kasar ta gaza wajen kare kiristoci daga ‘yan bindiga da ke zaune a yankin Arewa maso yamma.

Gwamnatin Nijeriya, ta musanta duk wani tsangwama ga kiristoci, tana mai cewa; tana kai wa ‘yan ta’adda da sauran kungiyoyi masu dauke da makamai hare-hare tare da kashe Kiristoci da Musulmai.

Rundunar sojin Amurka da ke da alhakin gudanar da ayyukanta a Afirka, rundunar sojin Amurka da ke Afirka ta ce; tana taimaka wa Nijeriya a yakin da ke da kungiyoyi masu tsattsauran ra’ayi da suka hada da kungiyar Boko Haram da kuma yankin yammacin Afirka.

Shugaban JIBWIS ya bukaci gwamnatin tarayya da ta fayyace alakar sojojin Amurka da Nijeriya,

Shugaban Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Ikamatis Sunnah (Jibwis) ta Kasa, Abdullahi Bala Lau, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi watsi da yarjejeniyoyin da suka kulla da Amurka dangane da batun tura sojojin Amurka Nijeriya.

Da yake zantawa a wata hira da ya yi BBC Hausa, Bala Lau ya ce; kasancewar Amurka kasa ce ta duniya da ke da manyan hanyoyin leken asiri, ya kamata ta rika tantance bayanai game da Nijeriya, maimakon dogaro da labaran da suke kunshe da siyasa a ciki.

Amurka
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Sabuwar Gobara Ta Sake Tashi A Kano, Ta Ƙone Shaguna 50

Sabuwar Gobara Ta Sake Tashi A Kano, Ta Ƙone Shaguna 50

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.