ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Za A Yankani Ba Zan Koma APC Ba – Gwamnan Bauchi 

by Leadership Hausa
6 months ago

Daga Khalid Idris Doya

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya zargi gwamnatin tarayya da amfani da hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa wajen musguna wa ‘yan adawa da ci musu mutunci, ya bayyana cewar saboda ya ƙi ya koma cikin APC ne ta masa bi ta da ƙulli. 

 

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya yi zargin ne bayan sanya hannu kan kasafin kuɗin jihar na 2026 a ranar Laraba, inda ya nuna cewa ko da yankashi za a yi ba zai taɓa komawa APC ba.

  • GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar Ta Samar Da Mafita Ga Kasashen Da Ke Cikin Mawuyacin Hali
  • Saƙon Sakatare Janar Na MDD, Antonio Guterres Na Shiga Sabuwar Skekarar 2026

Idan za a tuna dai EFCC ta cafke Kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi Yakubu Adamu da farko an zargi da hannu wajen almundahana da sama da Naira biliyan 5, sai kuma a ranar Laraba hukumar ta sake gurfanar da shi bisa sabon zargin da hannu a taimaka wa ayyukan ta’addanci ta hanyar tallafawa da kuɗaɗe.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

 

Gwamnan jihar Bauchi ya ce wasu gwamnoni sun koma APC bisa wasu dalilai, amma shi saboda ya ƙi komawa cikin APC ne ya sanya gwamamtin tarayya ke musguna masa.

 

“Wasu ‘yan uwa gwamnoni sun bar ni sun koma APC bisa waɗansu dalilai ni kuma na ƙi, sai ana ci min mutunci, ana cin mutunci ma’aikatana, ana cin mutunci iyalaina ana so a mana ƙazafi har ma da cewa muna cikin masu kawo harkokin ta’addanci; wanda babu ta’addanci a Bauchi, zaman lafiya ake yi.

 

“Kuma aka kawo sunan wani wai Bodejo wanda ƙanine a wajena kuma ba a nan garin ya ke ba, a Nasasawa ya ke. Kuma ba ni ya fara taimaka a siyasa ba; ya taimaki mai girma shugaban ƙasa, ya taimaki gwamnan Nasarawa, in ya na da matsala ba kawai za a haɗashi da shi da ni kawai don shi Bafulatani ba ne.

 

“Ni na riga na faɗa a baya. Duk wanda ya ci mutuncin Bafulatani saboda banbancin yare ba zan bar shi ba. Saboda haka na kare Badejo saboda na san ban taɓa ganinsa da ta’addanci ba.”

 

Gwamnan ya ce saboda kawai ana son a ɓata shi ne aka haɗashi da Bello Badejo saboda hasashen siyasa, ya nuna hakan da cewa ba daidai ba ne.

 

“An ɗauki kwamishina na an rufe shi an masa ƙazafofi iri-iri. Kuma a matsayina na gwamna ina da kariya na musamman bai kamata ake sanya sunana a cikin kotu ba. Ko wani abu na yi na kisa ma sai na sauƙa. Amma saboda ba su san gwamnati ba kuma gwamnatinsu na cin mutunci abun da suke yi kenan.

 

“Na yi shiru saboda ba na son mu yi maganganun da za su kawo fararraƙa ƙasa tun da ƙasar ma a ɓare ta ke. Ga talauci, ga yaudara, ga ƙarya, ga yunwa amma kullum ana ƙarya wa mutane. Ana karɓar bashi ba a san me ake yi da shi ba. Ana karɓar kashi 51 na kuɗin Nijeriya ba a san me ake yi da shi ba,” ya yi zargi.

 

Ya ƙara da cewa su kuɗaɗen da suke samu a jihohi suna aiki da su, sai ya yi zargin cewa wasu gwamnonin ba su aiki da kuɗaɗen da suke samu amma su ba a taɓa su.

 

“Sai mu da muke aikin ake taɓawa saboda ana duba kila a gaba za mu zama wani abu; zama wani abu ai na Allah ne.”

 

Ya ce adawa dole ne kuma babu wanda ya isa a tursasa masa fita a PDP domin ya koma APC, “Ko za su yankani ina inda na ke ni da mutanena. Mutanen Bauchi sun ce kar na je ko’ina.”

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Shugabannin Sin Da Rasha Sun Yi Musayar Gaisuwar Sabuwar Shekara

Shugabannin Sin Da Rasha Sun Yi Musayar Gaisuwar Sabuwar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.