ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Za A Yankani Ba Zan Koma APC Ba – Gwamnan Bauchi 

by Leadership Hausa
7 months ago

Daga Khalid Idris Doya

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya zargi gwamnatin tarayya da amfani da hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa wajen musguna wa ‘yan adawa da ci musu mutunci, ya bayyana cewar saboda ya ƙi ya koma cikin APC ne ta masa bi ta da ƙulli. 

 

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya yi zargin ne bayan sanya hannu kan kasafin kuɗin jihar na 2026 a ranar Laraba, inda ya nuna cewa ko da yankashi za a yi ba zai taɓa komawa APC ba.

  • GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar Ta Samar Da Mafita Ga Kasashen Da Ke Cikin Mawuyacin Hali
  • Saƙon Sakatare Janar Na MDD, Antonio Guterres Na Shiga Sabuwar Skekarar 2026

Idan za a tuna dai EFCC ta cafke Kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi Yakubu Adamu da farko an zargi da hannu wajen almundahana da sama da Naira biliyan 5, sai kuma a ranar Laraba hukumar ta sake gurfanar da shi bisa sabon zargin da hannu a taimaka wa ayyukan ta’addanci ta hanyar tallafawa da kuɗaɗe.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

 

Gwamnan jihar Bauchi ya ce wasu gwamnoni sun koma APC bisa wasu dalilai, amma shi saboda ya ƙi komawa cikin APC ne ya sanya gwamamtin tarayya ke musguna masa.

 

“Wasu ‘yan uwa gwamnoni sun bar ni sun koma APC bisa waɗansu dalilai ni kuma na ƙi, sai ana ci min mutunci, ana cin mutunci ma’aikatana, ana cin mutunci iyalaina ana so a mana ƙazafi har ma da cewa muna cikin masu kawo harkokin ta’addanci; wanda babu ta’addanci a Bauchi, zaman lafiya ake yi.

 

“Kuma aka kawo sunan wani wai Bodejo wanda ƙanine a wajena kuma ba a nan garin ya ke ba, a Nasasawa ya ke. Kuma ba ni ya fara taimaka a siyasa ba; ya taimaki mai girma shugaban ƙasa, ya taimaki gwamnan Nasarawa, in ya na da matsala ba kawai za a haɗashi da shi da ni kawai don shi Bafulatani ba ne.

 

“Ni na riga na faɗa a baya. Duk wanda ya ci mutuncin Bafulatani saboda banbancin yare ba zan bar shi ba. Saboda haka na kare Badejo saboda na san ban taɓa ganinsa da ta’addanci ba.”

 

Gwamnan ya ce saboda kawai ana son a ɓata shi ne aka haɗashi da Bello Badejo saboda hasashen siyasa, ya nuna hakan da cewa ba daidai ba ne.

 

“An ɗauki kwamishina na an rufe shi an masa ƙazafofi iri-iri. Kuma a matsayina na gwamna ina da kariya na musamman bai kamata ake sanya sunana a cikin kotu ba. Ko wani abu na yi na kisa ma sai na sauƙa. Amma saboda ba su san gwamnati ba kuma gwamnatinsu na cin mutunci abun da suke yi kenan.

 

“Na yi shiru saboda ba na son mu yi maganganun da za su kawo fararraƙa ƙasa tun da ƙasar ma a ɓare ta ke. Ga talauci, ga yaudara, ga ƙarya, ga yunwa amma kullum ana ƙarya wa mutane. Ana karɓar bashi ba a san me ake yi da shi ba. Ana karɓar kashi 51 na kuɗin Nijeriya ba a san me ake yi da shi ba,” ya yi zargi.

 

Ya ƙara da cewa su kuɗaɗen da suke samu a jihohi suna aiki da su, sai ya yi zargin cewa wasu gwamnonin ba su aiki da kuɗaɗen da suke samu amma su ba a taɓa su.

 

“Sai mu da muke aikin ake taɓawa saboda ana duba kila a gaba za mu zama wani abu; zama wani abu ai na Allah ne.”

 

Ya ce adawa dole ne kuma babu wanda ya isa a tursasa masa fita a PDP domin ya koma APC, “Ko za su yankani ina inda na ke ni da mutanena. Mutanen Bauchi sun ce kar na je ko’ina.”

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Shugabannin Sin Da Rasha Sun Yi Musayar Gaisuwar Sabuwar Shekara

Shugabannin Sin Da Rasha Sun Yi Musayar Gaisuwar Sabuwar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.