Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ya sanar da hukumomin tsaro game da shirinsa na gudanar da bukukuwan hawan sallar layya na shekarar 2026 daga fadarsa da ke Nasarawa.
A cikin wasiƙu daban-daban da aka aika wa Kwamishinan ƴansandan jihar Kano, Ibrahim Bakori, da Daraktan DSS na jihar, masarautar ta bayyana cewa an fara shirye-shiryen gudanar da bukukuwan Sallah da za su fara daga ranar 27 ga Mayu, 2026.
Wasiƙun, waɗanda aka sanya wa hannu daga sakataren Sarkin Kano, Abdullahi Kwaru, sun ce shawarar gudanar da hawan ta biyo bayan tarurrukan da majalisar masarautar Kano ta gudanar.
Masarautar ta bayyana cewa hawan wata muhimmiyar al’ada ce ta shekara-shekara da ke bai wa Sarki damar zagaya cikin birni tare da hakimai da sauran masu sarauta domin gaisawa da jama’a da karɓar gaisuwa daga talakawansa. Haka kuma ta tabbatar wa hukumomin tsaro cewa za a gudanar da bikin cikin lumana tare da neman haɗin kai da goyon bayansu.
Lamarin na zuwa ne yayin da ake ci gaba da nuna sha’awa kan shirye-shiryen hawa a Kano, musamman a daidai lokacin da ake ci gaba da taƙaddama a kotu kan sarautar Kano bayan gwamnatin jihar ta tuɓe Aminu Ado Bayero tare da mayar da Muhammadu Sanusi II kan karagar sarauta.















Discussion about this post