Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tabbatar da cewa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), na da ikon fitar da ƙa’idoji da jadawalin gudanar da zaɓe.
Mai shari’a James Omotosho ne, ya yanke hukuncin a ranar 26 ga watan Mayu, 2026, inda ya yi watsi da ƙarar da jam’iyyar SDP ta shigar domin ƙalubalantar ikon INEC.
Jam’iyyar ta ce INEC ba ta da ikon sanya ranakun gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen 2027.
Sai dai lauyan INEC, Alex Izinyon, ya bayyana wa kotu cewa kundin tsarin mulki da dokar zaɓe ta 2026 sun bai wa hukumar ikon tsara da gudanar da harkokin zaɓe tare da fitar da jadawalin zaɓe.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Omotosho ya amince da hujjar INEC tare da tabbatar da ikon hukumar wajen tsara da gudanar da zaɓen shekarar 2027.















Discussion about this post