Wata Kotun Musamman kan Laifuffuka da ke Ikeja a jihar Legas ta yanke wa wani fasto mai shekara 63, Chris Douglas, hukuncin ɗaurin rai da rai bayan samunsa da laifin fyaɗe ‘yar wani mamba na cocinsa. Alkali Rahman Oshodi ne ya yanke hukuncin a ranar Alhamis, inda ya tabbatar da laifin faston wanda shi ne babban mai kula da cocin Peculiar Generation Assembly da ke yankin Oshodi.
A cikin hukuncinsa, Alkali Oshodi ya ce wanda aka yankewa hukunci ya ci amanar matsayin sa na jagoran addini da amincewar da aka ba shi, inda ya yi anfani da yarinyar. Ya bayyana cewa iyalan yarinyar suna kallonsa a matsayin uba, amma ya karya wannan amana ta hanyar da bai dace ba. Kotun ta tabbatar da cewa an aikata laifin ne a wani otel sau da dama yayin da iyalan ke neman shiriya ta addini daga gare shi.
Kafa Kamfanin Sarrafa Gwal A Legas: Ƙungiyar Dattawan Arewa Ta Ƙalubalanci Tinubu
NPA Ta Ce Jiragen Ruwa 33 Ɗauke Da Kaya Sun Sauka A Tashohin Legas
Kotun ta kuma bayyana irin illar da abin ya haifar wa yarinyar ta fuskar tunani, inda ta fada cikin damuwa mai tsanani da kuma tunanin kashe kanta sakamakon abin da ya faru. A yayin shari’ar, masu gabatar da kara karkashin jagorancin Daraktan Shari’o’in Gwamnati, Dr. Babajide Martins, sun gabatar da shaidu guda biyar da suka hada da yarinyar, mahaifiyarta da likita, tare da gabatar da hujjoji na likitanci da takardu.
Ko da yake wanda aka yankewa hukuncin ya musanta zargin yana cewa sun yi ne da yardar juna, kotun ta yi watsi da wannan hujja tare da cewa an tabbatar da laifin fyade ba tare da wata shakka ba. Daga karshe, kotun ta wanke shi daga wasu tuhume-tuhume shida amma ta same shi da laifi a kan tuhume-tuhume uku na fyade, inda ta yanke masa hukuncin daurin rai da rai kan kowanne, tare da umarnin saka sunansa a rajistar masu aikata laifukan lalata ta jihar Legas.













Discussion about this post