ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Hukuncin Kisa Kan Wanda Ya Kashe ‘Yar Shekara 5 A Kano

by Leadership Hausa
8 months ago

Rabiu Ali Indabawa

Kotun Daukaka Kara da ke zama a Kano ta sake tabbatar da hukuncin kisa ta hanyar rataya da aka yanke wa Abdulmalik Tanko bisa laifin garkuwa da kuma kisan yarinya ‘yar shekara takwas, Hanifa Abubakar.

Mai Shari’a A.R. Muhammad, wanda ya karanta hukuncin a ranar Talata, ya yi watsi da karar da Tanko ya shigar, tare da tabbatar da hukuncin Kotun Babbar Jihar Kano, yana mai cewa kotun shari’ar farko ta yi aiki daidai da doka kuma ta tantance shaidu yadda ya kamata.

  • Gwamnan Gombe Ya Kafa Hukumar Kula Da Wutar Lantarki
  • Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji

A cewar Mai Shari’an, kotun daukaka karar ta gano cewa hujjojin da mai kara ya gabatar ba su da karfi, inda ta ce shaidun da masu kare hukuncin suka gabatar sun kasance masu karfi da gamsarwa.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, ya bayyana cewa babu wani dalili da zai sa a tsoma baki a hukuncin kotun kasa.

Mai Shari’a Muhammad ya kuma yi kira ga gwamnati da ta tabbatar an aiwatar da hukuncin bayan wanda aka yanke wa hukuncin ya kammala dukkan hanyoyin daukaka kara da doka ta tanada.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Rahoton LEADERSHIP ya bayyana cewa Hanifa Abubakar, ‘yar shekara biyar, an sace ta a watan Disamba 2021 da Abdulmalik Tanko, mamallakin makarantar Noble Kids Academy da ke Karamar Hukumar Nassarawa a Jihar Kano.

Tanko ya nemi kudin fansa Naira miliyan 6 daga iyayenta kafin daga bisani ya sanya mata guba ta bera, abin da ya yi sanadiyyar rasuwarta.

Lamarin ya jawo Allah-wadai daga sassa daban-daban na kasar nan, sakamakon karancin shekarun yarinyar da kuma cin amanar da aka yi, ganin cewa Tanko shi ne mamallakin makarantar da take karatu a cikinta.

An gurfanar da Tanko a gaban kotu a ranar 24 ga Janairu, 2022, tare da Isyaku Hashim da Fatima Jibril, kan tuhuma da suka shafi hada baki wajen aikata laifi, garkuwa da mutane, tsare mutum ba bisa ka’ida ba, da kuma kisan kai da gangan.

A ranar 28 ga Yuli, 2022, Kotun Babbar Jihar Kano, karkashin jagorancin Mai Shari’a Usman Na’abba, ta yanke wa wanda aka samu da laifi da kuma Hashim hukuncin kisa ta hanyar rataya, yayin da aka yanke wa Fatima Jibril hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Next Post
Ci Gaban Sin Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

Ci Gaban Sin Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.