ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Sun Ƙwace Haramtaccen Man Fetur A Jihohin Adamawa Da Taraba

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta kama man fetur da aka yi safararsa ba bisa ƙa’ida ba, fatun jakuna, da sauran haramtattun kayayyaki da darajarsu ta kai Naira miliyan 98.375 a jihohin Adamawa da Taraba cikin makonni shida.

Kwanturolan yankin, Mataimakin Kwanturola Janar Aminu Tako, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Laraba, inda ya danganta nasarar da aka samu da ci gaba da gudanar da ayyukan leƙen asiri domin daƙile safarar kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da kuma kare tattalin arziki.

  • Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Ya ce an kama kayayyakin ne a wurare daban-daban a jihohin biyu.

ADVERTISEMENT

“Ranar 26 ga Fabrairu, 2026, da misalin ƙarfe 1:10 na rana, jami’ai sun kama buhuna 43 na tufafin sawa na hannu na ƙasashen waje, da kuma kwalaye biyar da fakiti 12 na magungunan Ɓiagra 200mg a hanyar Saɓannah-Numan,” in ji shi.

Tako ya ƙara da cewa a ranar 12 ga Maris, 2026, jami’an sun ƙwace fatun jakuna guda 509 da kilo 460 na naman jakin da aka busar a hanyar Mubi-Sangere.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya kuma bayyana cewa a ranar 13 ga Maris, 2026, jami’ai sun kama jarkoki 110 na man fetur (PMS), kowanne ɗauke da lita 25, a hanyar Likitaba-Gembu a Jihar Taraba.

A cewarsa, ƙarin kayayyakin da aka kama sun haɗa da jarkoki 520 na PMS da jarkoki 112 na dizal (AGO) a hanyar Mubi-Sahuda a ranar 15 ga Maris, sannan jarkoki 482 na PMS a hanyar Maiha-Belel a ranar 17 ga Maris.

Ya ce sabuwar kama ta faru ne a ranar 11 ga Afrilu, 2026, lokacin da jami’ai suka kama jarkoki 176 da kuma ganguna uku masu ɗauke da lita 220-220 na PMS a hanyar Toungo-Ganye.

“Gaba ɗaya, an kama jarkoki 1,288 da ganguna uku ɗauke da kimanin lita 32,860 na PMS, tare da lita 2,800 na AGO da sauran kayayyaki, waɗanda jimillar darajarsu ta kai Naira 98,375,325,” in ji Tako.

Ya bayyana cewa an gudanar da wannan aiki ne bisa tanade-tanaden Dokar Hukumar Kwastam ta 2023, wadda ke bai wa hukumar damar hana fitar da kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da kuma ƙwace su.

Kwanturolan yankin ya gargaɗi cewa safarar man fetur, namun daji, da magungunan da ba su da rajista na haifar da barazana ga tsaron kasa, lafiyar jama’a, da kuma daidaiton tattalin arziki.

“Babu sassauci kan irin waɗannan laifuffuka a ƙarƙashin jagorancina. Duk wanda aka kama zai fuskanci ƙwace kayansa, kamawa da kuma gurfanar da shi a gaban kuliya ba tare da wata rangwame ba,” in ji shi.

Tako ya buƙaci masu harkar safarar kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da su koma kasuwanci na halal, yana mai jaddada cewa hukumar za ta ci gaba da tallafa wa kasuwanci na gaskiya tare da yaƙi da masu safarar kaya.

Ya kuma yaba wa Babban Kwanturola Janar na Kwastam, Adewale Adeniyi, da sauran hukumomin tsaro kan haɗin gwiwar da suke bayarwa wajen samun nasarar ayyuka.

An daɗe ana ganin yankunan kan iyaka na jihohin Adamawa da Taraba a matsayin manyan hanyoyin safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba, saboda kusancinsu da kasashen waje da kuma yanayin ƙasa mai wahala.

A ƴan shekarun nan, Hukumar Kwastam ta ƙara tsaurara sa ido da aiwatar da dokoki domin daƙile safarar man fetur zuwa kasashen makwabta, inda ake sayar da shi da farashi mai tsada don samun riba.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Nazarin Yadda Jiragen Saman Yaƙin Sojoji Ke Ci Gaba Kashe Fararen Hula A Nijeriya

Nazarin Yadda Jiragen Saman Yaƙin Sojoji Ke Ci Gaba Kashe Fararen Hula A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.