ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Sun Ƙwace Haramtaccen Man Fetur A Jihohin Adamawa Da Taraba

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago

Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta kama man fetur da aka yi safararsa ba bisa ƙa’ida ba, fatun jakuna, da sauran haramtattun kayayyaki da darajarsu ta kai Naira miliyan 98.375 a jihohin Adamawa da Taraba cikin makonni shida.

Kwanturolan yankin, Mataimakin Kwanturola Janar Aminu Tako, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Laraba, inda ya danganta nasarar da aka samu da ci gaba da gudanar da ayyukan leƙen asiri domin daƙile safarar kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da kuma kare tattalin arziki.

  • ‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano
  • Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

Ya ce an kama kayayyakin ne a wurare daban-daban a jihohin biyu.

ADVERTISEMENT

“Ranar 26 ga Fabrairu, 2026, da misalin ƙarfe 1:10 na rana, jami’ai sun kama buhuna 43 na tufafin sawa na hannu na ƙasashen waje, da kuma kwalaye biyar da fakiti 12 na magungunan Ɓiagra 200mg a hanyar Saɓannah-Numan,” in ji shi.

Tako ya ƙara da cewa a ranar 12 ga Maris, 2026, jami’an sun ƙwace fatun jakuna guda 509 da kilo 460 na naman jakin da aka busar a hanyar Mubi-Sangere.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Ya kuma bayyana cewa a ranar 13 ga Maris, 2026, jami’ai sun kama jarkoki 110 na man fetur (PMS), kowanne ɗauke da lita 25, a hanyar Likitaba-Gembu a Jihar Taraba.

A cewarsa, ƙarin kayayyakin da aka kama sun haɗa da jarkoki 520 na PMS da jarkoki 112 na dizal (AGO) a hanyar Mubi-Sahuda a ranar 15 ga Maris, sannan jarkoki 482 na PMS a hanyar Maiha-Belel a ranar 17 ga Maris.

Ya ce sabuwar kama ta faru ne a ranar 11 ga Afrilu, 2026, lokacin da jami’ai suka kama jarkoki 176 da kuma ganguna uku masu ɗauke da lita 220-220 na PMS a hanyar Toungo-Ganye.

“Gaba ɗaya, an kama jarkoki 1,288 da ganguna uku ɗauke da kimanin lita 32,860 na PMS, tare da lita 2,800 na AGO da sauran kayayyaki, waɗanda jimillar darajarsu ta kai Naira 98,375,325,” in ji Tako.

Ya bayyana cewa an gudanar da wannan aiki ne bisa tanade-tanaden Dokar Hukumar Kwastam ta 2023, wadda ke bai wa hukumar damar hana fitar da kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da kuma ƙwace su.

Kwanturolan yankin ya gargaɗi cewa safarar man fetur, namun daji, da magungunan da ba su da rajista na haifar da barazana ga tsaron kasa, lafiyar jama’a, da kuma daidaiton tattalin arziki.

“Babu sassauci kan irin waɗannan laifuffuka a ƙarƙashin jagorancina. Duk wanda aka kama zai fuskanci ƙwace kayansa, kamawa da kuma gurfanar da shi a gaban kuliya ba tare da wata rangwame ba,” in ji shi.

Tako ya buƙaci masu harkar safarar kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da su koma kasuwanci na halal, yana mai jaddada cewa hukumar za ta ci gaba da tallafa wa kasuwanci na gaskiya tare da yaƙi da masu safarar kaya.

Ya kuma yaba wa Babban Kwanturola Janar na Kwastam, Adewale Adeniyi, da sauran hukumomin tsaro kan haɗin gwiwar da suke bayarwa wajen samun nasarar ayyuka.

An daɗe ana ganin yankunan kan iyaka na jihohin Adamawa da Taraba a matsayin manyan hanyoyin safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba, saboda kusancinsu da kasashen waje da kuma yanayin ƙasa mai wahala.

A ƴan shekarun nan, Hukumar Kwastam ta ƙara tsaurara sa ido da aiwatar da dokoki domin daƙile safarar man fetur zuwa kasashen makwabta, inda ake sayar da shi da farashi mai tsada don samun riba.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Nazarin Yadda Jiragen Saman Yaƙin Sojoji Ke Ci Gaba Kashe Fararen Hula A Nijeriya

Nazarin Yadda Jiragen Saman Yaƙin Sojoji Ke Ci Gaba Kashe Fararen Hula A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.