Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta kama man fetur da aka yi safararsa ba bisa ƙa’ida ba, fatun jakuna, da sauran haramtattun kayayyaki da darajarsu ta kai Naira miliyan 98.375 a jihohin Adamawa da Taraba cikin makonni shida.
Kwanturolan yankin, Mataimakin Kwanturola Janar Aminu Tako, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Laraba, inda ya danganta nasarar da aka samu da ci gaba da gudanar da ayyukan leƙen asiri domin daƙile safarar kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da kuma kare tattalin arziki.
- Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
- Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
- Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
- Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
- Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Ya ce an kama kayayyakin ne a wurare daban-daban a jihohin biyu.
“Ranar 26 ga Fabrairu, 2026, da misalin ƙarfe 1:10 na rana, jami’ai sun kama buhuna 43 na tufafin sawa na hannu na ƙasashen waje, da kuma kwalaye biyar da fakiti 12 na magungunan Ɓiagra 200mg a hanyar Saɓannah-Numan,” in ji shi.
Tako ya ƙara da cewa a ranar 12 ga Maris, 2026, jami’an sun ƙwace fatun jakuna guda 509 da kilo 460 na naman jakin da aka busar a hanyar Mubi-Sangere.
Ya kuma bayyana cewa a ranar 13 ga Maris, 2026, jami’ai sun kama jarkoki 110 na man fetur (PMS), kowanne ɗauke da lita 25, a hanyar Likitaba-Gembu a Jihar Taraba.
A cewarsa, ƙarin kayayyakin da aka kama sun haɗa da jarkoki 520 na PMS da jarkoki 112 na dizal (AGO) a hanyar Mubi-Sahuda a ranar 15 ga Maris, sannan jarkoki 482 na PMS a hanyar Maiha-Belel a ranar 17 ga Maris.
Ya ce sabuwar kama ta faru ne a ranar 11 ga Afrilu, 2026, lokacin da jami’ai suka kama jarkoki 176 da kuma ganguna uku masu ɗauke da lita 220-220 na PMS a hanyar Toungo-Ganye.
“Gaba ɗaya, an kama jarkoki 1,288 da ganguna uku ɗauke da kimanin lita 32,860 na PMS, tare da lita 2,800 na AGO da sauran kayayyaki, waɗanda jimillar darajarsu ta kai Naira 98,375,325,” in ji Tako.
Ya bayyana cewa an gudanar da wannan aiki ne bisa tanade-tanaden Dokar Hukumar Kwastam ta 2023, wadda ke bai wa hukumar damar hana fitar da kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da kuma ƙwace su.
Kwanturolan yankin ya gargaɗi cewa safarar man fetur, namun daji, da magungunan da ba su da rajista na haifar da barazana ga tsaron kasa, lafiyar jama’a, da kuma daidaiton tattalin arziki.
“Babu sassauci kan irin waɗannan laifuffuka a ƙarƙashin jagorancina. Duk wanda aka kama zai fuskanci ƙwace kayansa, kamawa da kuma gurfanar da shi a gaban kuliya ba tare da wata rangwame ba,” in ji shi.
Tako ya buƙaci masu harkar safarar kayayyaki ba bisa ƙa’ida ba da su koma kasuwanci na halal, yana mai jaddada cewa hukumar za ta ci gaba da tallafa wa kasuwanci na gaskiya tare da yaƙi da masu safarar kaya.
Ya kuma yaba wa Babban Kwanturola Janar na Kwastam, Adewale Adeniyi, da sauran hukumomin tsaro kan haɗin gwiwar da suke bayarwa wajen samun nasarar ayyuka.
An daɗe ana ganin yankunan kan iyaka na jihohin Adamawa da Taraba a matsayin manyan hanyoyin safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba, saboda kusancinsu da kasashen waje da kuma yanayin ƙasa mai wahala.
A ƴan shekarun nan, Hukumar Kwastam ta ƙara tsaurara sa ido da aiwatar da dokoki domin daƙile safarar man fetur zuwa kasashen makwabta, inda ake sayar da shi da farashi mai tsada don samun riba.















Discussion about this post